ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
10 months ago
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ajandar ci gaban da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa ta ƙunshi dukkan sassan ƙasar ba tare da nuna ɓangaranci ba, inda ake gudanar da manyan ayyuka da shirye-shirye a faɗin ƙasa.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana haka ne a Abuja ranar Laraba, lokacin da ya karɓi baƙuncin Kwamishinonin Yaɗa Labarai na jihohi 36.

ADVERTISEMENT
  • Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

“Ya ce: “Ban taɓa ganin inda ake da ayyukan yi amma Shugaban Ƙasa ya ƙi aiwatarwa saboda gwamnan wannan jiha ba ya cikin APC ba. A duk abin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hankalinsa yana kan ɗan Nijeriya ne.”

 

LABARAI MASU NASABA

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Dangane da cire tallafin man fetur kuwa, ya ce hakan ya bai wa jihohi damar samun kuɗaɗe fiye da da domin aiwatar da ayyuka masu muhimmanci.

 

Ya ce: “Cire tallafin man fetur ya buɗe hanya da ta bai wa dukkan shugabanninku damar aiwatar da ayyuka da kawo wa jama’a amfanin dimokuraɗiyya. Ban ji wani gwamna ba, ko daga jam’iyyarmu ko wata jam’iyya, da ya ce mu dawo da tsohon tsarin.”

 

Idris ya tunatar da cewa kafin Tinubu ya hau mulki, jihohi 27 na fama da biyan albashi, sannan kashi 97 na kuɗaɗen shiga na ƙasa na tafiya wajen biyan bashi. Amma yanzu, a cewarsa, an samu sauyi saboda gyare-gyaren da Shugaban Ƙasa ya aiwatar.

 

Ya ce: “Nijeriya na kan tafiya zuwa ga ci gaba na dindindin da zai amfani kowa. Saƙona, da kuma saƙon da muke da shi a gare ku duka shi ne ku zo ku shiga wannan jirgi domin kai Nijeriya ga inda Shugaban Ƙasa ya yi alƙawarin kai ta, kuma wanda kuke so ku gani a ƙarshe.”

 

Haka kuma, Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya za ta kai ziyara wasu jihohin Kudu maso Kudu da Arewa maso Gabas domin duba manyan ayyuka tare da tattaunawa da jama’a a matsayin wani ɓangare na tsarin samun ra’ayin jama’a.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Kwamishinonin Yaɗa Labarai, wanda kuma shi ne Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Borno, Farfesa Usman Tar, ya ce za su yi aiki tare ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasa ba, domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da inganta ƙimomin al’umma.

 

Ya ce: “A gabanka akwai kwamishinoni daga jam’iyyun siyasa daban-daban, daga yankuna daban-daban na ƙasar nan. Saboda haka muna wakiltar sassa daban-daban na tarayyar Nijeriya. Ba mu zo a madadin wata jam’iyya ko wani muradi na kashin kai ba. Mun zo ne bisa wani dandali na ƙasa domin tattauna hanyoyi da dabarun inganta muradinmu na ƙasa, ɗabi’unmu da kuma wayar da kanmu”

 

Ya ƙara da cewa ƙungiyar tasu za ta ci gaba da goyon bayan ma’aikatar wajen yaɗa muhimman kamfen na ƙasa, ciki har da wayar da kai da tarukan tattaunawa da jama’a.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

MASU ALAKA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Labarai

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.