ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
10 months ago
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ajandar ci gaban da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa ta ƙunshi dukkan sassan ƙasar ba tare da nuna ɓangaranci ba, inda ake gudanar da manyan ayyuka da shirye-shirye a faɗin ƙasa.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana haka ne a Abuja ranar Laraba, lokacin da ya karɓi baƙuncin Kwamishinonin Yaɗa Labarai na jihohi 36.

ADVERTISEMENT
  • Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

“Ya ce: “Ban taɓa ganin inda ake da ayyukan yi amma Shugaban Ƙasa ya ƙi aiwatarwa saboda gwamnan wannan jiha ba ya cikin APC ba. A duk abin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hankalinsa yana kan ɗan Nijeriya ne.”

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Dangane da cire tallafin man fetur kuwa, ya ce hakan ya bai wa jihohi damar samun kuɗaɗe fiye da da domin aiwatar da ayyuka masu muhimmanci.

 

Ya ce: “Cire tallafin man fetur ya buɗe hanya da ta bai wa dukkan shugabanninku damar aiwatar da ayyuka da kawo wa jama’a amfanin dimokuraɗiyya. Ban ji wani gwamna ba, ko daga jam’iyyarmu ko wata jam’iyya, da ya ce mu dawo da tsohon tsarin.”

 

Idris ya tunatar da cewa kafin Tinubu ya hau mulki, jihohi 27 na fama da biyan albashi, sannan kashi 97 na kuɗaɗen shiga na ƙasa na tafiya wajen biyan bashi. Amma yanzu, a cewarsa, an samu sauyi saboda gyare-gyaren da Shugaban Ƙasa ya aiwatar.

 

Ya ce: “Nijeriya na kan tafiya zuwa ga ci gaba na dindindin da zai amfani kowa. Saƙona, da kuma saƙon da muke da shi a gare ku duka shi ne ku zo ku shiga wannan jirgi domin kai Nijeriya ga inda Shugaban Ƙasa ya yi alƙawarin kai ta, kuma wanda kuke so ku gani a ƙarshe.”

 

Haka kuma, Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya za ta kai ziyara wasu jihohin Kudu maso Kudu da Arewa maso Gabas domin duba manyan ayyuka tare da tattaunawa da jama’a a matsayin wani ɓangare na tsarin samun ra’ayin jama’a.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Kwamishinonin Yaɗa Labarai, wanda kuma shi ne Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Borno, Farfesa Usman Tar, ya ce za su yi aiki tare ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasa ba, domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da inganta ƙimomin al’umma.

 

Ya ce: “A gabanka akwai kwamishinoni daga jam’iyyun siyasa daban-daban, daga yankuna daban-daban na ƙasar nan. Saboda haka muna wakiltar sassa daban-daban na tarayyar Nijeriya. Ba mu zo a madadin wata jam’iyya ko wani muradi na kashin kai ba. Mun zo ne bisa wani dandali na ƙasa domin tattauna hanyoyi da dabarun inganta muradinmu na ƙasa, ɗabi’unmu da kuma wayar da kanmu”

 

Ya ƙara da cewa ƙungiyar tasu za ta ci gaba da goyon bayan ma’aikatar wajen yaɗa muhimman kamfen na ƙasa, ciki har da wayar da kai da tarukan tattaunawa da jama’a.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.