• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Samoa: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Hukuncin NMCC Kan Zargin Auren Jinsi

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta yaba wa Hukumar Yaƙi Da Ƙorafe-ƙorafen Yaɗa Labarai ta Ƙasa (National Media Complaints Commission, NMCC), mai kula da harkokin yaɗa labarai a Nijeriya, kan hukuncin da ta yanke a kan wata jarida dangane da rahoton bogi da ta buga dangane da yarjejeniyar Samoa.

 

a wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman ga Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayar, gwamnatin ta ce, hukuncin ya nuna muhimmancin tabbatar da gaskiya da riƙon amana, tare da tunatar da ‘yan jarida irin muhimmiyar rawar da suke takawa wajen yin tasiri kan fahimtar jama’a ta hanyar bayar da rahotanni na gaskiya.

  • Hadimin Tinubu Ya Raba Kayayyakin Makaranta Ga Daliban Firamare A Kano
  • Zargin Ta’addanci A Zamfara: Matawalle Ya Ƙalubalanci Gwamna Dauda Su Yi Rantsuwa Da Alƙur’ani

Haka kuma, ta jaddada cewa dole ne kafafen yaɗa labarai su bi ƙa’idojin aiki don guje wa rahotanni masu cutarwa.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Da take amincewa da ‘yan jarida a matsayin ginshiƙan dimokuraɗiyya, gwamnatin ta yi nuni da cewa, ‘yancin ‘yan jarida yana tafiya ne tare da alhakin bayar da rahotannin gaskiya.

 

Ta kuma yaba da shawarar NMCC ta cewa, tilas ne jaridar ta bai wa jama’a haƙuri tare da kuma ɗaukar matakan hana faruwar irin wannan lamarin a nan gaba.

 

Ta ce: “An yi la’akari da kiran da aka yi ga hukumomin Gwamnatin Tarayya da su ƙara fayyace gaskiya, kuma za a ɗauki matakai don ganin an sanar da ‘yan Nijeriya isassun abubuwan da suka shafi jama’a.”

 

Ta ƙara da cewa, “Gwamnatin Tarayya ta himmatu wajen samar da yanayin da kafafen yaɗa labarai ke bunƙasa tare da ci gaba da bin ƙa’idojin ɗa’a na ma’aikatar.

 

“Muna kira ga dukkan kafafen watsa labarai da su ci gaba da kiyaye waɗannan ƙa’idoji kuma su yi aiki tare wajen yaɗa sahihan bayanai, waɗanda ke da muhimmanci ga ‘yan ƙasa.”

 

Gwamnati ta yi fatan wannan hukunci zai zama wani ma’auni na hazaƙar aikin jarida a Nijeriya, da kuma ƙarfafa danƙon zumunci tsakanin kafafen yaɗa labarai da gwamnati, da al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Varane Ya Yi Ritaya Daga Buga Kwallon Kafa Yanada Shekara 31

Next Post

Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al’ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

2 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

3 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

5 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

6 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

9 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

10 hours ago
Next Post
Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al’ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

Kwastam Za Ta Haɗa Gwiwa Da Al'ummomin Kan Iyakoki Wajen Daƙile Yaɗuwar Makamai

LABARAI MASU NASABA

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.