Ayau ranar Alhamis ce ake sa ran kotun koli zata raba gardama kan wanda yake da sahihancin tsaya takara a kujerar gwamna a karkashin Jam’iyyar APC a Jihar Jigawa.
Umar Namadi ta bakin lauyansa, Prince Lateef Fagbemi (SAN) ya yi nasara a babbar kotun tarayya da ke Dutse da kuma kotun daukaka kara da ke Kano.
Amma, Aliyu, bisa daukaka karar da ya shigar mai lamba: SC/1453/2022 yana kalubalantar hukuncin da Kotun Daukaka Kara (reshen Kano) ta yanke a ranar 4 ga Nuwamba, 2022 wadda ta yi watsi da karar da ya shigar a baya tare da tabbatar da zaben Namadi a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar Jigawa. .
Kwamitin mutum uku karkashin jagorancin Mai shari’a Ita Mbaba, a hukuncin da aka yanke ranar 4 ga watan Nuwamba, ya yi watsi da daukaka karar da Aliyu ya shigar a kan hukuncin ranar 13 ga Satumba, 2022 da mai shari’a Hassan Dikko na babbar kotun tarayya da ke Dutse, ya yi kan rashin bayar da hujjoji kwarara.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp