• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Tabeel

Sakamakon matakan soja da Isra’ila ta fara daukawa tun watan Oktoban bara, Palasdinawa sama da miliyan biyu aka raba da muhallansu a zirin Gaza, ciki har da yarinya mai suna Sama Tabeel da iyalanta. 

 

Wata rana da daddare, sojojin Isra’ila sun kai hari inda Sama da iyalanta ke gudun hijira a yankin Rafah, amma Sama da iyalanta sun taki sa’a sun tsira daga fashewar bama-bamai da wargajewar gine-gine, kuma kashegari sun bar Rafah sun tashi zuwa Khan Younis. Amma sakamakon tsananin gigita Sama da harin ya yi, gashin kanta ya fara zubewa. Duk da cewa iyayenta sun yi iyakacin kokarin neman mata magani, amma sun gaza, sakamakon yadda ake matukar fuskantar matsalar karancin magani da likita a Gaza.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano
  • Sauƙaƙa Farashin Man Fetur: Matatar Ɗangote Za Ta Gana Da ‘Yan Kasuwa A Ranar Talata 

Sama da shekara guda ke nan da barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, amma maimakon kurar rikicin ya lafa, sai kara yaduwa take yi, har zuwa sauran kasashen yankin gabas ta tsakiya, ciki har da Lebanon da Syria da Iran da sauransu, lamarin da ya jefa al’ummomin kasashen cikin mawuyacin hali. Kawo yanzu, Palasdinawa sama da dubu 42 suka halaka baya ga kusan dubu 100 da suka jikkata a zirin Gaza a sakamakon rikicin, sai kuma a Lebanon, mutane sama da 2000 suka mutu baya ga wasu sama da dubu 10 suka ji raunuka… A sa’i daya kuma, fararen hula sama da dubu daya suka jikkata a Isra’ila, a yayin da daruruwan sojojin kasar suka halaka.

 

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Kamata ya yi bangarorin da rikicin ya shafa da ma gamayyar kasa da kasa su yi tunani sosai a kan cewa, shin me ya haifar da tushen kiyayya da juna a shiyyar? Baya ga haka, a yayin da halin da ake ciki ke dada ta’azzara a yankin gabas ta tsakiya, kasashe da dama sun yi ta kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta, kuma sau da yawa kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da kuma babban taron majalisar sun kira taro game da yanayin da ake ciki a zirin Gaza da Lebanon da kuma gabas ta tsakiya, don fatan ganin an tabbatar da tsagaita bude wuta. Amma ita kasar Amurka a maimakon ta yi kokarin sanyaya yanayin da ake ciki, sai ta yi ta rura wutar rikicin, wadda sau da dama ta jefa kuri’ar kin amincewa da daftarin shirin tsagaita bude wuta da aka gabatar a kwamitin sulhu na MDD, har ma ta yi ta samar da makamai ga Isra’ila, ko a karshen watan Satumba, Amurka ta kara samar da gudummawar soja da ta kai kimanin dala biliyan 8.7 ga Isra’ila. Lallai, yadda kasashen yamma suka bi ma’aunai biyu a kan batun, shi ma ya haifar da tasiri ga aukuwar rikici a yankin gabas ta tsakiya.

 

Abubuwan da ke faruwa a gabas ta tsakiya sun shaida cewa, daukar matakan soja da nuna karfin tuwo ba za su taimaka ga daidaita matsala ba. Abin da ake bukata wajen daidaita rikicin Palasdinu da Isra’ila shi ne niyyar siyasa da kuma daukar matakan diplomasiyya, a maimakon makamai da kuma daukar matakan takunkumi. Kamata ya yi manyan kasashe su taka rawar da ta dace, su kiyaye adalci, don kwantar kurar yaki da shawo kan yaduwar rikicin.

 

Ba da jimawa ba, kasar Sin ta bayar da shawarar daidaita rikicin Gaza bisa wasu matakai uku, wato na farko a gaggauta tsagaita bude wuta da samar da agajin jin kai, sa’an nan, a bi ka’idar ba Palasdinawa ikon gudanar da harkokinsu da kansu, daga karshe, shirin samar da kasashe biyu zai zama ainihin mafita ta warware matsalar. Kamata ya yi kasa da kasa su sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, sa’an nan su tsara taswirar aiwatar da shirin, don tabbatar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, da Larabawa da kuma Yahudawa.

 

Sama da shekara guda ke nan, ba a ko taba ganin alamar zaman lafiya a Gaza ba, ga shi yanzu Lebanon ma ta tsunduma cikin yaki. Shin yaushe ne za a maido da zaman lafiya a gabas ta tsakiya? Kuma yaushe ne za a fitar da yara irinsu Sama Tabeel daga fargabar da aka jefa su a ciki? (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
Next Post
Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.