• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon matakan soja da Isra’ila ta fara daukawa tun watan Oktoban bara, Palasdinawa sama da miliyan biyu aka raba da muhallansu a zirin Gaza, ciki har da yarinya mai suna Sama Tabeel da iyalanta. 

 

Wata rana da daddare, sojojin Isra’ila sun kai hari inda Sama da iyalanta ke gudun hijira a yankin Rafah, amma Sama da iyalanta sun taki sa’a sun tsira daga fashewar bama-bamai da wargajewar gine-gine, kuma kashegari sun bar Rafah sun tashi zuwa Khan Younis. Amma sakamakon tsananin gigita Sama da harin ya yi, gashin kanta ya fara zubewa. Duk da cewa iyayenta sun yi iyakacin kokarin neman mata magani, amma sun gaza, sakamakon yadda ake matukar fuskantar matsalar karancin magani da likita a Gaza.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano
  • Sauƙaƙa Farashin Man Fetur: Matatar Ɗangote Za Ta Gana Da ‘Yan Kasuwa A Ranar Talata 

Sama da shekara guda ke nan da barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, amma maimakon kurar rikicin ya lafa, sai kara yaduwa take yi, har zuwa sauran kasashen yankin gabas ta tsakiya, ciki har da Lebanon da Syria da Iran da sauransu, lamarin da ya jefa al’ummomin kasashen cikin mawuyacin hali. Kawo yanzu, Palasdinawa sama da dubu 42 suka halaka baya ga kusan dubu 100 da suka jikkata a zirin Gaza a sakamakon rikicin, sai kuma a Lebanon, mutane sama da 2000 suka mutu baya ga wasu sama da dubu 10 suka ji raunuka… A sa’i daya kuma, fararen hula sama da dubu daya suka jikkata a Isra’ila, a yayin da daruruwan sojojin kasar suka halaka.

 

Labarai Masu Nasaba

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Kamata ya yi bangarorin da rikicin ya shafa da ma gamayyar kasa da kasa su yi tunani sosai a kan cewa, shin me ya haifar da tushen kiyayya da juna a shiyyar? Baya ga haka, a yayin da halin da ake ciki ke dada ta’azzara a yankin gabas ta tsakiya, kasashe da dama sun yi ta kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta, kuma sau da yawa kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da kuma babban taron majalisar sun kira taro game da yanayin da ake ciki a zirin Gaza da Lebanon da kuma gabas ta tsakiya, don fatan ganin an tabbatar da tsagaita bude wuta. Amma ita kasar Amurka a maimakon ta yi kokarin sanyaya yanayin da ake ciki, sai ta yi ta rura wutar rikicin, wadda sau da dama ta jefa kuri’ar kin amincewa da daftarin shirin tsagaita bude wuta da aka gabatar a kwamitin sulhu na MDD, har ma ta yi ta samar da makamai ga Isra’ila, ko a karshen watan Satumba, Amurka ta kara samar da gudummawar soja da ta kai kimanin dala biliyan 8.7 ga Isra’ila. Lallai, yadda kasashen yamma suka bi ma’aunai biyu a kan batun, shi ma ya haifar da tasiri ga aukuwar rikici a yankin gabas ta tsakiya.

 

Abubuwan da ke faruwa a gabas ta tsakiya sun shaida cewa, daukar matakan soja da nuna karfin tuwo ba za su taimaka ga daidaita matsala ba. Abin da ake bukata wajen daidaita rikicin Palasdinu da Isra’ila shi ne niyyar siyasa da kuma daukar matakan diplomasiyya, a maimakon makamai da kuma daukar matakan takunkumi. Kamata ya yi manyan kasashe su taka rawar da ta dace, su kiyaye adalci, don kwantar kurar yaki da shawo kan yaduwar rikicin.

 

Ba da jimawa ba, kasar Sin ta bayar da shawarar daidaita rikicin Gaza bisa wasu matakai uku, wato na farko a gaggauta tsagaita bude wuta da samar da agajin jin kai, sa’an nan, a bi ka’idar ba Palasdinawa ikon gudanar da harkokinsu da kansu, daga karshe, shirin samar da kasashe biyu zai zama ainihin mafita ta warware matsalar. Kamata ya yi kasa da kasa su sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, sa’an nan su tsara taswirar aiwatar da shirin, don tabbatar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, da Larabawa da kuma Yahudawa.

 

Sama da shekara guda ke nan, ba a ko taba ganin alamar zaman lafiya a Gaza ba, ga shi yanzu Lebanon ma ta tsunduma cikin yaki. Shin yaushe ne za a maido da zaman lafiya a gabas ta tsakiya? Kuma yaushe ne za a fitar da yara irinsu Sama Tabeel daga fargabar da aka jefa su a ciki? (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Next Post

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Related

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

1 week ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 weeks ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 weeks ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

3 weeks ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

3 weeks ago
Next Post
Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.