ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Tabeel

Sakamakon matakan soja da Isra’ila ta fara daukawa tun watan Oktoban bara, Palasdinawa sama da miliyan biyu aka raba da muhallansu a zirin Gaza, ciki har da yarinya mai suna Sama Tabeel da iyalanta. 

 

Wata rana da daddare, sojojin Isra’ila sun kai hari inda Sama da iyalanta ke gudun hijira a yankin Rafah, amma Sama da iyalanta sun taki sa’a sun tsira daga fashewar bama-bamai da wargajewar gine-gine, kuma kashegari sun bar Rafah sun tashi zuwa Khan Younis. Amma sakamakon tsananin gigita Sama da harin ya yi, gashin kanta ya fara zubewa. Duk da cewa iyayenta sun yi iyakacin kokarin neman mata magani, amma sun gaza, sakamakon yadda ake matukar fuskantar matsalar karancin magani da likita a Gaza.

ADVERTISEMENT
  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano
  • Sauƙaƙa Farashin Man Fetur: Matatar Ɗangote Za Ta Gana Da ‘Yan Kasuwa A Ranar Talata 

Sama da shekara guda ke nan da barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, amma maimakon kurar rikicin ya lafa, sai kara yaduwa take yi, har zuwa sauran kasashen yankin gabas ta tsakiya, ciki har da Lebanon da Syria da Iran da sauransu, lamarin da ya jefa al’ummomin kasashen cikin mawuyacin hali. Kawo yanzu, Palasdinawa sama da dubu 42 suka halaka baya ga kusan dubu 100 da suka jikkata a zirin Gaza a sakamakon rikicin, sai kuma a Lebanon, mutane sama da 2000 suka mutu baya ga wasu sama da dubu 10 suka ji raunuka… A sa’i daya kuma, fararen hula sama da dubu daya suka jikkata a Isra’ila, a yayin da daruruwan sojojin kasar suka halaka.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Kamata ya yi bangarorin da rikicin ya shafa da ma gamayyar kasa da kasa su yi tunani sosai a kan cewa, shin me ya haifar da tushen kiyayya da juna a shiyyar? Baya ga haka, a yayin da halin da ake ciki ke dada ta’azzara a yankin gabas ta tsakiya, kasashe da dama sun yi ta kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta, kuma sau da yawa kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da kuma babban taron majalisar sun kira taro game da yanayin da ake ciki a zirin Gaza da Lebanon da kuma gabas ta tsakiya, don fatan ganin an tabbatar da tsagaita bude wuta. Amma ita kasar Amurka a maimakon ta yi kokarin sanyaya yanayin da ake ciki, sai ta yi ta rura wutar rikicin, wadda sau da dama ta jefa kuri’ar kin amincewa da daftarin shirin tsagaita bude wuta da aka gabatar a kwamitin sulhu na MDD, har ma ta yi ta samar da makamai ga Isra’ila, ko a karshen watan Satumba, Amurka ta kara samar da gudummawar soja da ta kai kimanin dala biliyan 8.7 ga Isra’ila. Lallai, yadda kasashen yamma suka bi ma’aunai biyu a kan batun, shi ma ya haifar da tasiri ga aukuwar rikici a yankin gabas ta tsakiya.

 

Abubuwan da ke faruwa a gabas ta tsakiya sun shaida cewa, daukar matakan soja da nuna karfin tuwo ba za su taimaka ga daidaita matsala ba. Abin da ake bukata wajen daidaita rikicin Palasdinu da Isra’ila shi ne niyyar siyasa da kuma daukar matakan diplomasiyya, a maimakon makamai da kuma daukar matakan takunkumi. Kamata ya yi manyan kasashe su taka rawar da ta dace, su kiyaye adalci, don kwantar kurar yaki da shawo kan yaduwar rikicin.

 

Ba da jimawa ba, kasar Sin ta bayar da shawarar daidaita rikicin Gaza bisa wasu matakai uku, wato na farko a gaggauta tsagaita bude wuta da samar da agajin jin kai, sa’an nan, a bi ka’idar ba Palasdinawa ikon gudanar da harkokinsu da kansu, daga karshe, shirin samar da kasashe biyu zai zama ainihin mafita ta warware matsalar. Kamata ya yi kasa da kasa su sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, sa’an nan su tsara taswirar aiwatar da shirin, don tabbatar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, da Larabawa da kuma Yahudawa.

 

Sama da shekara guda ke nan, ba a ko taba ganin alamar zaman lafiya a Gaza ba, ga shi yanzu Lebanon ma ta tsunduma cikin yaki. Shin yaushe ne za a maido da zaman lafiya a gabas ta tsakiya? Kuma yaushe ne za a fitar da yara irinsu Sama Tabeel daga fargabar da aka jefa su a ciki? (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

Tabeel
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Tabeel
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.