• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yaushe Ne Za A Fitar Da Sama Tabeel Daga Fargaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon matakan soja da Isra’ila ta fara daukawa tun watan Oktoban bara, Palasdinawa sama da miliyan biyu aka raba da muhallansu a zirin Gaza, ciki har da yarinya mai suna Sama Tabeel da iyalanta. 

 

Wata rana da daddare, sojojin Isra’ila sun kai hari inda Sama da iyalanta ke gudun hijira a yankin Rafah, amma Sama da iyalanta sun taki sa’a sun tsira daga fashewar bama-bamai da wargajewar gine-gine, kuma kashegari sun bar Rafah sun tashi zuwa Khan Younis. Amma sakamakon tsananin gigita Sama da harin ya yi, gashin kanta ya fara zubewa. Duk da cewa iyayenta sun yi iyakacin kokarin neman mata magani, amma sun gaza, sakamakon yadda ake matukar fuskantar matsalar karancin magani da likita a Gaza.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano
  • Sauƙaƙa Farashin Man Fetur: Matatar Ɗangote Za Ta Gana Da ‘Yan Kasuwa A Ranar Talata 

Sama da shekara guda ke nan da barkewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, amma maimakon kurar rikicin ya lafa, sai kara yaduwa take yi, har zuwa sauran kasashen yankin gabas ta tsakiya, ciki har da Lebanon da Syria da Iran da sauransu, lamarin da ya jefa al’ummomin kasashen cikin mawuyacin hali. Kawo yanzu, Palasdinawa sama da dubu 42 suka halaka baya ga kusan dubu 100 da suka jikkata a zirin Gaza a sakamakon rikicin, sai kuma a Lebanon, mutane sama da 2000 suka mutu baya ga wasu sama da dubu 10 suka ji raunuka… A sa’i daya kuma, fararen hula sama da dubu daya suka jikkata a Isra’ila, a yayin da daruruwan sojojin kasar suka halaka.

 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Kamata ya yi bangarorin da rikicin ya shafa da ma gamayyar kasa da kasa su yi tunani sosai a kan cewa, shin me ya haifar da tushen kiyayya da juna a shiyyar? Baya ga haka, a yayin da halin da ake ciki ke dada ta’azzara a yankin gabas ta tsakiya, kasashe da dama sun yi ta kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su tsagaita bude wuta, kuma sau da yawa kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da kuma babban taron majalisar sun kira taro game da yanayin da ake ciki a zirin Gaza da Lebanon da kuma gabas ta tsakiya, don fatan ganin an tabbatar da tsagaita bude wuta. Amma ita kasar Amurka a maimakon ta yi kokarin sanyaya yanayin da ake ciki, sai ta yi ta rura wutar rikicin, wadda sau da dama ta jefa kuri’ar kin amincewa da daftarin shirin tsagaita bude wuta da aka gabatar a kwamitin sulhu na MDD, har ma ta yi ta samar da makamai ga Isra’ila, ko a karshen watan Satumba, Amurka ta kara samar da gudummawar soja da ta kai kimanin dala biliyan 8.7 ga Isra’ila. Lallai, yadda kasashen yamma suka bi ma’aunai biyu a kan batun, shi ma ya haifar da tasiri ga aukuwar rikici a yankin gabas ta tsakiya.

 

Abubuwan da ke faruwa a gabas ta tsakiya sun shaida cewa, daukar matakan soja da nuna karfin tuwo ba za su taimaka ga daidaita matsala ba. Abin da ake bukata wajen daidaita rikicin Palasdinu da Isra’ila shi ne niyyar siyasa da kuma daukar matakan diplomasiyya, a maimakon makamai da kuma daukar matakan takunkumi. Kamata ya yi manyan kasashe su taka rawar da ta dace, su kiyaye adalci, don kwantar kurar yaki da shawo kan yaduwar rikicin.

 

Ba da jimawa ba, kasar Sin ta bayar da shawarar daidaita rikicin Gaza bisa wasu matakai uku, wato na farko a gaggauta tsagaita bude wuta da samar da agajin jin kai, sa’an nan, a bi ka’idar ba Palasdinawa ikon gudanar da harkokinsu da kansu, daga karshe, shirin samar da kasashe biyu zai zama ainihin mafita ta warware matsalar. Kamata ya yi kasa da kasa su sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, sa’an nan su tsara taswirar aiwatar da shirin, don tabbatar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, da Larabawa da kuma Yahudawa.

 

Sama da shekara guda ke nan, ba a ko taba ganin alamar zaman lafiya a Gaza ba, ga shi yanzu Lebanon ma ta tsunduma cikin yaki. Shin yaushe ne za a maido da zaman lafiya a gabas ta tsakiya? Kuma yaushe ne za a fitar da yara irinsu Sama Tabeel daga fargabar da aka jefa su a ciki? (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Next Post

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

5 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

1 week ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

Sin Za Ta Kara Karfin Kare Kauyukan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.