• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…

by Shehu Yahaya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Al’ummar Jihar Kaduna na ci gaba da zaman zulumi; bisa karuwar rashin tsaro, lamarin da ya tilasta wa wasu barin garuruwansu ba tare da sun shirya ba.

Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa, karshen ‘yan ta’adda ne ya zo, musamman ganin yadda jami’an tsaron Nijeriya suka datse hanyoyin da ke da hadaka da junansu a dazukan da suke zama da kuma karancin makamai da suke fama da shi yanzu.

  • Sin Za Ta Inganta Zamanintarwa Bisa Bunkasuwa Mai Inganci Don Ba Da Karin Karfi Ga Ci Gaban Duniya
  • Majasirdin Sarkin Zazzau, Alhaji Yusuf Saleh Barde Ya Rasu

Hasali ma sun bayyana cewa, yawaitar garkuwa da mutane a Jihar Kaduna, wata alamace da ke nuna cewa kwanakin ‘yan ta’addan sun zo karshe a jihar kamar yadda suka shaida wa LEADERSHIP Hausa.

Har ila yau kuma, wasu na ganin Gwamnatin Jihar Kaduna; karkashin jagorancin Sanata Uba Sani, na da matukar sassaucin ra’ayi wajen yaki da wadannan ‘yan ta’adda, sabanin gwamnatin da ta shude ta Malam Nasiru El-Rufa’i; wacce ta rika yin fito-na-fito da masu tayar da kayar-baya a jihar.

Wakilinmu, ya yi kokarin jin ta bakin Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Lamuran Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwa, domin jin irin matakan da suke dauka wajen samar da tsaro a fadin jihar, amma abin ya ci tura. Duk da haka, wakilinmu bai yi kasa a guiwa ba; domin kuwa ya tura masa sakon tes, bai ba da amsa ba, haka nan kuma ya kai ziyara ofishinsa; nan ma bai samu damar ganawa da shi ba.

A wata ganawa da hukumomin tsaro a jihar ta Kaduna kwanan na, Gwamna Uba Sani ya yi kira da a kaddamar da tsarin tsaro na bai-daya, ta hanyar inganta cudanya da jama’a gami da wayar da kan al’ummar; kan muhimmacin samar da tsaro.

Bugu da kari, Gwamna Uba Sani ya sha alwashin samar da dukkanin kayan aikin da suka dace ga hukumomin na tsaro, domin samun damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata a fadin jihar ta Kaduna baki-daya.

A zantawarsa da wakilinmu,  Dakta Yahuza Getso; masanin tsaro a Nijeriya da kasashen Afirka ya bayyana cewa, matsalar rashin tsaro a Jihar Kaduna; abubuwa ne guda hudu: “Abu na farko shi ne, dole ne sai jami’an tsaro sun tashi tsaye wajen tabbatar da dakatar da wadannan hare-hare da ake kaiwa, duk kuwa da cewa; jami’an tsaron suna yi bakin kokarinsu wajen kai hari ga ‘yan ta’addan, wanda hakan ya sanya su kuma ‘yan ta’addan suka tunzura tare da kai hare-hare a kan al’ummar da ba su ji ba, ba su kuma gani ba.

“Abu na biyu shi ne, akwai abin da masu iya magana ke cewa,  ‘Tusa ta kusa kure wa Bodari’, dalili kuwa, yanzu haka karfin wadannan ‘yan ta’adda ya yi matukar raguwa, sakamakon hana shiga da kayan masarufi na rayuwa da kuma takura musu da aka yi wajen ci gaba da samun makaman da suke yin ta’addanci da su, saboda idan ka dubi irin yadda suke kawo hare-hare a halin yanzu, ba sa zuwa da makamai duk da cewa suna diban mutane da dama.

“Abu na uku kuma shi ne, jami’an tsaro sun datse hanyoyin da suke samun hadaka da junansu, inda suke kai komo a cikin dazukan, saboda haka; sai suke ganin babu wata mafita sai dai su rika daukar mutane masu yawa, wanda hakan zai jawo hankalin hukumomi ko da za a kai musu hari; za a koma tunanin cewa akwai wasu mutane masu a tare da su masu yawan gaske, don haka wajibi ne a daga kafa wajen kai musu farmaki.

“Kazalika, abu na hudu shi ne;  idan aka ci gaba da samun bayanai daga al’umma, babu shakka jami’an tsaron sojojin wannan kasa, za su kakkabe kafatanin wAdannan ‘yan ta’adda.

“Batun da suke yi yanzu na neman kudin fansa, wanda kowa ya sani cewa ya wuce hankali, abu ne wanda suke yi domin kara razana al’umma da kuma jefa musu zaman zuLlumi, amma su shugabannin jami’an tsaron Nijeriya, suna kara samun kaimi ne idan suka ji ‘yan ta’addan na neman irin wadannan makudan mudade, wanda hakan ke nuna cewa; lallai karfinsu ya fara karewa; suna neman kudin sayen makamai da sauran makamantansu”.

“Saboda haka, mafita kadai yanzu ita ce; shugabanni su kara jin tsoron Allah, sannan kuma su tuna irin nauyin da Allah ya dora musu, wanda zai tambaye su wata rana. Haka nan, su ma jami’an tsaron; su kara kaimi tare da sanin cewa, wannan yaki da suke yi da ‘yan ta’adda; wata rana ko shakka babu za a kai ga cimma gaci. Saboda haka, ka da su samu sanyin guiwa a kan irin fadi tashin da ake yi, sannan kuma dole ne a kara dankon zumunta tre da fahimtar juna a tsakanin jami’an tsaro da sauran al’umma, wanda hakan zai taimaka wajen samun bayanan sirri da kuma sa ido, domin kara taimakawa wajen samun nasarar yakin da ake yi wajen kawar da wadannan ‘yan ta’adda a fadin yankin baki-daya”, in ji Dakta Getso.

A nashi bangaren, Malam Muhammad Garba, Tsohon Malamin Makaranta ne a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya da ke Kaduna, sannan kuma mai yin fashin baki a kan harkokin siyasar ta Jihar Kaduna ya bayyan cewa, akwai hasashen da ake yi cewa, Gwamnatin Uba Sani; na da sassauci a kan harkokin tsaro, lamarin da ake ganin shi ne silar samun yawaitar matsalar rashin tsaron a fadin jihar.

“Lokacin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i; ya hana kowa sakat, domin kuwa ya yi amfani da wasu bangarori na jami’an tsaro tare da sa ido a kowane lungu da sako, ya kuma kokarin tarwatsa wadannan ‘yan ta’adda; har sai da ta kai ga babu wani mai iya yin  motsi a jihar.

Wannan dalili ne, ya sa aka samu saukin yawaitar ire-iren wadannan hare-hare na ‘yan ta’adda a fadin jihar, amma yanzu ana ganin wannan gwamnatin ta Uba Sani, tana da matukar sassauci;” in ji shi.

Jibrin Aliyu Kuriga (Dan Bala), mazaunin garin Kuriga ne da ke cikin Karamar Hukumar Chikun da ke Jihar Kaduna, ya bayyana cewa, shi ne mutum na farko da ‘yan bindigar suka fara yin garkuwa da shi a tarihin wannan gari, inda ya kwashe kimanin kwanaki 53 a hannunsu; kafin da aka biya kudin fansa ya shaki iskar ‘yanci, a cewar tasa; “Wallahi cikin kwanaki 53 da na kwashe a hannunsu, ban taba sa ruwa na wanke fuskata da shi ba; haka nan duk hannayena sun sha duka, wanda ban taba tunanin za su ci gaba da aiki a gaba ba”.

 “Mu tara aka kwashe, amma bayan an yi sulhu da ‘yan bindigar daga baya sai suka sako mutum biyar; sauran hudun kuma suka kashe su. Saboda haka, mu al’ummar Jihar Kaduna; musamman mu da muke yin rayuwa a wajen jihar, shakka babu rayuwarmu na cikin wani mayuwacin hali na zaman zulumi, bisa wannan matsalar ta rashin tsaro da muke fama da ita,” a ta bakinsa.

Wani mai sana’ar sayar da Gawayi a Jihar Kaduna, Malam Abdulkarim Jibrin, ya bayyana cewa,  ko shakka babu rashin tsaro ya shafi sana’ar kasuwancinsu, musamman su da suke shiga kauyuka suna gudanar da kasuwancinsu, wanda a halin yanzu ‘yan ta’adda duk sun ta da wadannan kauyuka baki-daya.

“Duk inda za ka je ka sayo itace da gawayi, yanzu babu sakamakon tashin kauyakan da ‘yan ta’addar suka yi, sannan kuma ai duk garin da a yau aka ce babu kauye, ya zama nakasasshe komai girmansa. Mu dai yanzu, wanzuwar ‘yan bindiga ya taba rayuwarmu da ta iyalinmu “.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Gillar Sojoji 17: Tinubu Ya Shafa Wa Idonsa Toka, Sojoji Sun Kai Mamaya

Next Post

Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

Related

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

6 hours ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

7 hours ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

8 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

10 hours ago
Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano
Manyan Labarai

Namadi Sambo Ya Yaba Wa Gwamna Abba Yusuf Kan Bunƙasa Ɓangaren Ilimi Da Gine-Gine A Kano

11 hours ago
China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
Manyan Labarai

China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS

13 hours ago
Next Post
Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.