ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

by Bello Hamza, Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
Tinubu
  • Majalisa Za Ta Gudanar Da Bincike
  • Dukkan Ɓangarori Ne Ke Ɗanɗanawa – MURIC

 

Mai bai wa Shugaban Kasa Bola Tinubu Shawara na Musamman kan Harkokin Yada Labarai da Sadarwa, Sunday Dare, ya karyata zargin da Sanatan Amurka Ted Cruz, mai gabatar da shirye-shiryen talabijin Bill Maher, da mai sharhi kan harkokin siyasa Ban Jones suka yi cewa ana gudanar da “kisan kiyashi ga Kiristoci” a Nijeriya.

 

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na D (wanda a da ake kira Twitter) a ranar Litinin, mai taken “Karyata Maganar Kisan Kiyashi da Sanata Ted Cruz, Bill Maher, Ban Jones da sauran su suka yada,” Dare ya bayyana wannan zargi a matsayin karya, abin yaudara, kuma mai iya haifar da rarrabuwar kai.

  • Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
  • An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

Ya zargi masu sharhin daga kasashen waje da “kirkirar zarge-zargen ban mamaki game da wani kisan kiyashi da ba a tabbatar da shi ba,” yana kira ga ’yan Nijeriya da al’ummar duniya su yi watsi da wannan yunkuri na “sanya wa kasar riga wadda ba ta dace da ita ba.”

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

 

Dare ya jaddada cewa Nijeriya kasa ce mai addinai da dama, wacce aka gina bisa juriya, zaman lafiya, da girmama juna tsakanin mabambantan addinai, al’ummomin da ya ce Tinubu ya shugabanta.

 

Dare ya ambaci maganar Shugaban Kasa inda ya jaddada cewa Nijeriya “kasa ce mai cikakken ‘yanci da girma, wadda aka gina bisa bangaskiya da juriyar jama’arta,” ya kara da cewa “Babu wani addini da ake zalunta, kuma babu wata al’umma da aka ware.”

Yana nuna misali da rayuwar Shugaban Kasa a matsayin shaida ta juriya da fahimtar addinai, Dare ya bayyana cewa Shugaba Tinubu, Musulmi ne da yake auren fasto mai bin addinin Kirista.

Ya kuma ruwaito Shugaban yana cewa, “Gaba da kiyayya ba su da gurbi a gare mu. Soyayya ce abin da muke wa’azanta, kuma dole mu rika son juna.”

Dare ya bayyana cewa labarin “kisan kiyashi ga Kiristoci” babban rudani ne da ya kau da kai daga ainihin matsalolin tsaro da Nijeriya ke fama da su, inda ya bayyana cewa kasar na yaki da ta’addanci da ‘yan fashi da ke yin barna don samun riba da tayar da hankali, ba saboda addini ba.

Ya ce, “Wadannan ‘yan ta’adda suna kai hari kan fararen hula ba tare da bambance coci-coci, masallatai, kasuwanni, makarantu ko kauyuka ba, suna kashe ’yan Nijeriya masu bin addinai da kabilu daban-daban.”

Ya yi gargadin cewa fassara wannan rikici a matsayin yakin addini yana kara karfafa ’yan ta’adda ne tare da raunana hadin kan kasa.

Ya yi kira ga Cruz, Maher da sauran su da su nemi sahihan bayanai kafin su yada karya da ke bata sunan Nijeriya tare da karfafa ’yan ta’adda.

Dare ya kammala da cewa, “Gaskiya abu daya ce mai sauki , Nijeriya ba ta fuskantar kisan kiyashi ga Kiristoci; tana yaki ne da ta’addanci da ke kai hari ga kowa da kowa. Duk wanda ya yi zargi, to ya gabatar da hujja.”

A wani bangaren kuma majalisar dattawa ta zartar da kudurin tattauna lamarin da zaran sun kama aiki gadan-gadan daga hutun da suka dawo ranar Talata da ta gabata. Wannan na zuwa ne bayan da Sanata Ali Ndume da Sanata Sani Musa da Sanata Aliyu Wamakko da kuma Sanata Ibrahim Bomai suka gabatar da kudurin neman haka ga zauren majalisar ranar Talata.

A cikin kudurin da suka gabatar, sanatocin sun nemi bangarorin gwamnati da suke da ruwa da tsaki a kan lamarin musamman ma’aikatar kasashen waje da hukumomin tsaro su tabbatar da bayar da kididdiga da bayanai da suka kamata don karyata wannan frofaganda na kafafen yada labarai na kasashen waje suke neman bata sunan Nijeriya a idon kasashen duniya.

Sanata Ndume ya nuna damuwarsa na yadda ake yada labaran kanzon kurege a kan halin tsaron da kasar nan ke fuskanta. Yana mai cewa, dukkan bangarorin al’umma ke dandana matsalar rikicin ba wai wasu addinai ko kabilu ba.

Wani mai wasan barkwanci na kasar Amurka ne dai mai suna Bill Maher, ya yi ikirarin cewa, an kashe fiye da Kiristoci 100,000 a kisan kare dandi da ake yi wa Kiristocin Nijeriya.

Haka kuma wasu kugiyoyin musulmai kamar MURIC ta bayyana cewa, ayyukan ‘yan ta’adda a Nijeriya a cikin shekararun ya shafi duk wani dan Nijeriya ta hanyoyi daban daban. Haka kuma an tabbatar da cewa, lamarin ya ci rayukan musulmai fiye da 32,000 a cikin shekara uku. Don haka dukkan bangarorin ‘yan Nijeriya ke dandanawa” ya kuma kamata a hada hannu gaba daya don kawo karshen ayyukkan ‘yan ta’adda” in ji kungiyar.

Tinubu
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Tinubu
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.