• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Taurarin Da Muke Gani A Sama Na Raguwa Duk Shekara

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labarai
0
Yawan Taurarin Da Muke Gani A Sama Na Raguwa Duk Shekara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawan taurarin da mutane ke gani da idanunsu yana raguwa a hankali cikin shekara 10 da ta gabata.

Wannan kuwa ya faru ne sakamakon hasken da ke mamaye samaniya na fitilun da muke kunnawa a duniya – kuma tun 2011 hasken da ake samu na fitilu a duniya ke karuwa a kowacce shekara.

Dakta Christopher Kyba, wani masanin kimiyya ne a cibiyar bincike kan duniya ta Potsdam da ke Jamus, ya shaida wa BBC cewa: ” Taurarin da muke gani na raguwa”.
Shi da abokan aikinsa sun wallafa wannan bincike a jaridarsu ta kimiyya.

Wannan shi ne karshen binciken wasu masu koyon nazarin ilimin taurari da masana kimiyya na tsawon shekara 12, wadanda suke fita da daddare suna kirga taurarin da ke sama.

Rahoton da mutanen suka kammala na intanet da ake kira Globe at Night, ya mayar da hankali kan sauyin da ake samu na ganin taurari a samaniya – kuma ya yi daidai da karin kashi 10 cikin 100 da ake samu na hasken duniya a kowacce shekara.

Labarai Masu Nasaba

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wannan na nufin, yaron da aka haifa a yankin da ake iya ganin taurari 250 a sama, akwai yiwuwar nan da shekara 18 ba zai iya ganin ko taurari 100 ba a yankin.

Tiririn gurbatacciyar hasken duniya
Idan aka yi nazari kan bayanin da masu binciken nan Fabio Falchi da Salbador Bará, suka wallafa a jarida game da tiririn hasken duniya sun ce : “idan muka duba bidiyon da hukumar sararin samaniya take nunawa da kuma hotuna na duniyarmu da daddare, “Kyan hasken birane ne ke rudar mutane”, kai ka ce hasken bishiyar Kirsimeti ne.
“Ba su gane illar da ke cikin hoton ta gurbatar da hasken ke samarwa ba.
Kawai sun fi mayar da hankali ne kan kyan hoton da nau’in kalolin da suke da shi irin wanda ake gani a cikin ruwa, ba su lura da cewa tiririn gurbatattun sinadarai ne da ke tattare a cikin hasken wutar ba.
“Dakta Kyba, ya ce yana fatan ganin an samu ci gaba ta fuskar gurbatar da haske yake samar wa a ‘yan shekarun nan, saboda yawancin manyan birane suna sauya tsarin hasken da suke amfani da shi zuwa na makamashin da ba ya gurbata muhalli.
Garuruwa da birane musamman a kasashen da suka ci gaba, suna sauya fitilun kan titi zuwa masu aiki da hasken rana.
“Fatan shi ne idan za a yi amfani da wutar da ta dace, yanayin zai habaka ya yi kyau,” in ji shi.
Amma da wadannan fitilun da muke aiki da su – da yiwuwar mu sake gurbata hasken samaniyar da muke da shi.
Hukumar ta yi bayanin cewa “Cin karon da ake samu na hasken” da ake samu, ya sanya aka bullo da hasken da ake kira LED da alkawarin zai rage yawan amfani da makamashi, sannan kuma ya kara karfin gani ga bil’adama da daddare, amma hasken karuwa ma yake.
Idan aka samu cin karon da aka samu, shi ne a alkawarin sauki da kuma inganta kyau da zai yi, musamman ga al’umar da suka saba da hasken wuta.”Yawan hasken da ake samu shi ba iya illar rage taurari ya tsaya ba. Yana illa ga lafiyar dan ‘Adam da kuma tsarin yadda yake barci.
Yana haifar da matsala ga yanayin halayyar dabbobin da ba sa bacci da daddare, wanda a bayan nan wani bincike ya nuna ana samun raguwar kwari.
Shi tiririn hasken asara ce ga makamashi. Kuma kullum ci gaba muke da haska makamashi cikin sammai, wanda hakan ba daidai ba ne, in ji Daktan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Firayin Ministan Thailand: Sake Fara Ziyarar Sinawa Masu Yawon Shakatawa A Thailand Na Da Babbar Ma’ana

Next Post

Abin Da Zai Sa Na Amince Da Shan Kaye A 2023 – Kwankwaso

Related

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

2 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

4 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

7 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

18 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

24 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

1 day ago
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Abin Da Zai Sa Na Amince Da Shan Kaye A 2023 – Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.