ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Taurarin Da Muke Gani A Sama Na Raguwa Duk Shekara

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago

Yawan taurarin da mutane ke gani da idanunsu yana raguwa a hankali cikin shekara 10 da ta gabata.

Wannan kuwa ya faru ne sakamakon hasken da ke mamaye samaniya na fitilun da muke kunnawa a duniya – kuma tun 2011 hasken da ake samu na fitilu a duniya ke karuwa a kowacce shekara.

Dakta Christopher Kyba, wani masanin kimiyya ne a cibiyar bincike kan duniya ta Potsdam da ke Jamus, ya shaida wa BBC cewa: ” Taurarin da muke gani na raguwa”.
Shi da abokan aikinsa sun wallafa wannan bincike a jaridarsu ta kimiyya.

ADVERTISEMENT

Wannan shi ne karshen binciken wasu masu koyon nazarin ilimin taurari da masana kimiyya na tsawon shekara 12, wadanda suke fita da daddare suna kirga taurarin da ke sama.

Rahoton da mutanen suka kammala na intanet da ake kira Globe at Night, ya mayar da hankali kan sauyin da ake samu na ganin taurari a samaniya – kuma ya yi daidai da karin kashi 10 cikin 100 da ake samu na hasken duniya a kowacce shekara.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Wannan na nufin, yaron da aka haifa a yankin da ake iya ganin taurari 250 a sama, akwai yiwuwar nan da shekara 18 ba zai iya ganin ko taurari 100 ba a yankin.

Tiririn gurbatacciyar hasken duniya
Idan aka yi nazari kan bayanin da masu binciken nan Fabio Falchi da Salbador Bará, suka wallafa a jarida game da tiririn hasken duniya sun ce : “idan muka duba bidiyon da hukumar sararin samaniya take nunawa da kuma hotuna na duniyarmu da daddare, “Kyan hasken birane ne ke rudar mutane”, kai ka ce hasken bishiyar Kirsimeti ne.
“Ba su gane illar da ke cikin hoton ta gurbatar da hasken ke samarwa ba.
Kawai sun fi mayar da hankali ne kan kyan hoton da nau’in kalolin da suke da shi irin wanda ake gani a cikin ruwa, ba su lura da cewa tiririn gurbatattun sinadarai ne da ke tattare a cikin hasken wutar ba.
“Dakta Kyba, ya ce yana fatan ganin an samu ci gaba ta fuskar gurbatar da haske yake samar wa a ‘yan shekarun nan, saboda yawancin manyan birane suna sauya tsarin hasken da suke amfani da shi zuwa na makamashin da ba ya gurbata muhalli.
Garuruwa da birane musamman a kasashen da suka ci gaba, suna sauya fitilun kan titi zuwa masu aiki da hasken rana.
“Fatan shi ne idan za a yi amfani da wutar da ta dace, yanayin zai habaka ya yi kyau,” in ji shi.
Amma da wadannan fitilun da muke aiki da su – da yiwuwar mu sake gurbata hasken samaniyar da muke da shi.
Hukumar ta yi bayanin cewa “Cin karon da ake samu na hasken” da ake samu, ya sanya aka bullo da hasken da ake kira LED da alkawarin zai rage yawan amfani da makamashi, sannan kuma ya kara karfin gani ga bil’adama da daddare, amma hasken karuwa ma yake.
Idan aka samu cin karon da aka samu, shi ne a alkawarin sauki da kuma inganta kyau da zai yi, musamman ga al’umar da suka saba da hasken wuta.”Yawan hasken da ake samu shi ba iya illar rage taurari ya tsaya ba. Yana illa ga lafiyar dan ‘Adam da kuma tsarin yadda yake barci.
Yana haifar da matsala ga yanayin halayyar dabbobin da ba sa bacci da daddare, wanda a bayan nan wani bincike ya nuna ana samun raguwar kwari.
Shi tiririn hasken asara ce ga makamashi. Kuma kullum ci gaba muke da haska makamashi cikin sammai, wanda hakan ba daidai ba ne, in ji Daktan.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

MASU ALAKA

Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Labarai

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
Labarai

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Next Post
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Abin Da Zai Sa Na Amince Da Shan Kaye A 2023 – Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.