• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Gwamna A Jihohi 3: INEC Ta Wallafa Cikakken Bayanan Katittikan Masu Zaɓe

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Zaɓen Gwamna A Jihohi 3: INEC Ta Wallafa Cikakken Bayanan Katittikan Masu Zaɓe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC) ta wallafa cikakken bayanai kan katittikan masu zaɓe (PVC) da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa a shirye-shiryen gudanar da zaɓuɓɓukan gwamna da za a yi a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi a ranar Asabar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Hakan ya biyo bayan taron da hukumar ta yi a ranar Litinin domin sake nazarin shirye-shiryen da ta ke yi na zaɓuɓɓukan gwamna da za a yi a jihohin uku.

  • Rikicin Gaza Ya Haifar Da Rashin Tabbas a Kasuwar Mai ta Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Kan Raya Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Tsakanin Sin Da Girka

A sanarwar da Babban Kwamishina kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Da Ilmantar Da Masu Zaɓe na INEC, Mista Sam Olumekun, ya rattabawa hannu, hukumar ta ce: “Kamar yadda aka yi a zaɓuɓɓukan baya-bayan nan, ciki har da Babban Zaben Mayun 2023, hukumar ta wallafa cikakken bayani kan katittikan masu zaɓe (PVC) da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa ba a jihohin uku a matakin rumfunan zaɓe.

“Haka kuma bayanin ya bada yadda aka rarraba rumfunan zaɓen a Yankunan Ƙananan Hukumomi, Mazaɓu, da sunayen rumfunan zaɓen, da alƙaluman lambobinsu, da yawan masu zaɓe da su ka yi rajista, da kuma yawan katittikan masu zaɓe da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa ba.

“Lissafin na jihohin uku ya nuna cewa daga cikin masu zaɓe 1,056,862 da su ka yi rajista a Jihar Bayelsa, mutum 1,017,613 sun karɓi katittikansu, 39, 249 ba a karba ba. A Jihar Imo, masu zaɓe da su ka yi rajista sun kai 2,419,922, mutum 2,318,919 sun karɓi katittikansu, sai 101,0003 da ba su karɓa ba, yayin da a Jihar Kogi, daga cikin masu zaɓe 1,932,654 da su ka yi rajista, mutum 1,833,160 sun karɓi katittikansu, sannan 99,494 ba su karɓa ba.”

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Hukumar ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a lamarin zaɓuɓɓukan da su yi la’akari da cewa, duk fa wata ƙuri’a da aka samu a rumfar zaɓe wadda ta haura yawan ƙuri’un da aka karɓa to shaida ce cewar an yi aringizo kuri’u.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECZaɓen gwamnonin kudu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Yankan Baya: Tinubu Ya Jadda Amincewarsa Da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa

Next Post

Gobe Laraba Za A Fara Sayar Da Tikitin Jirgin Ƙasa Ta Shafin Intanet – Minista

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

9 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
Gobe Laraba Za A Fara Sayar Da Tikitin Jirgin Ƙasa Ta Shafin Intanet – Minista

Gobe Laraba Za A Fara Sayar Da Tikitin Jirgin Ƙasa Ta Shafin Intanet – Minista

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.