ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Gwamna A Jihohi 3: INEC Ta Wallafa Cikakken Bayanan Katittikan Masu Zaɓe

by Sulaiman
3 years ago
Inec

Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta Ƙasa (INEC) ta wallafa cikakken bayanai kan katittikan masu zaɓe (PVC) da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa a shirye-shiryen gudanar da zaɓuɓɓukan gwamna da za a yi a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi a ranar Asabar 11 ga watan Nuwamban 2023.

Hakan ya biyo bayan taron da hukumar ta yi a ranar Litinin domin sake nazarin shirye-shiryen da ta ke yi na zaɓuɓɓukan gwamna da za a yi a jihohin uku.

  • Rikicin Gaza Ya Haifar Da Rashin Tabbas a Kasuwar Mai ta Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Kan Raya Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Tsakanin Sin Da Girka

A sanarwar da Babban Kwamishina kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Da Ilmantar Da Masu Zaɓe na INEC, Mista Sam Olumekun, ya rattabawa hannu, hukumar ta ce: “Kamar yadda aka yi a zaɓuɓɓukan baya-bayan nan, ciki har da Babban Zaben Mayun 2023, hukumar ta wallafa cikakken bayani kan katittikan masu zaɓe (PVC) da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa ba a jihohin uku a matakin rumfunan zaɓe.

ADVERTISEMENT

“Haka kuma bayanin ya bada yadda aka rarraba rumfunan zaɓen a Yankunan Ƙananan Hukumomi, Mazaɓu, da sunayen rumfunan zaɓen, da alƙaluman lambobinsu, da yawan masu zaɓe da su ka yi rajista, da kuma yawan katittikan masu zaɓe da aka karɓa da waɗanda ba a karɓa ba.

“Lissafin na jihohin uku ya nuna cewa daga cikin masu zaɓe 1,056,862 da su ka yi rajista a Jihar Bayelsa, mutum 1,017,613 sun karɓi katittikansu, 39, 249 ba a karba ba. A Jihar Imo, masu zaɓe da su ka yi rajista sun kai 2,419,922, mutum 2,318,919 sun karɓi katittikansu, sai 101,0003 da ba su karɓa ba, yayin da a Jihar Kogi, daga cikin masu zaɓe 1,932,654 da su ka yi rajista, mutum 1,833,160 sun karɓi katittikansu, sannan 99,494 ba su karɓa ba.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Hukumar ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a lamarin zaɓuɓɓukan da su yi la’akari da cewa, duk fa wata ƙuri’a da aka samu a rumfar zaɓe wadda ta haura yawan ƙuri’un da aka karɓa to shaida ce cewar an yi aringizo kuri’u.

Inec
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Gobe Laraba Za A Fara Sayar Da Tikitin Jirgin Ƙasa Ta Shafin Intanet – Minista

Gobe Laraba Za A Fara Sayar Da Tikitin Jirgin Ƙasa Ta Shafin Intanet – Minista

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.