• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a, 12 ga Mayu, 2023 Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta kafe sunayen ‘yan takarar da za su fafata a zaɓuɓɓukan gwamna na cike girbi da za a yi a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi.

 

Hukumar ta yi kira ga jama’a da su yi wa sunayen karatun ta-natsu domin gano idan wani ɗan takara ya ba da bayanin bogi game da kan shi domin ɗaukar mataki.

  • Ina Kammala Wa’adin Mulkina Na Biyu Zan Yi Ritaya Daga Siyasa – Gwamna Sule

Babban Kwamishina kuma shugaban kwamitin wayar da kan jama’a kan al’amurran zaɓe na INEC, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa ga manema labarai da ya rattaba wa hannu.

 

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

A ranar 25 ga Oktoba, 2022 ne dai hukumar ta fitar da jadawalin ayyuka da tsare-tsaren da za a aiwatar a zaɓuɓɓuka uku na cike gurbi na gwamnonin jihohin waɗanda za a gudanar a ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023.

 

Jam’iyyun siyasa sun gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwani kamar yadda doka ta tanada, kuma sun wallafa sunayen ‘yan takarar su da mataimakan su tare da bayanan su a gidan yanar da hukumar ta tanada domin ɗora irin waɗannan hotunan da bayanan kafin wa’adin karfe 6 na yamma na ranar 5 ga Mayu ya cika.

 

Dukkan jam’iyyu 18 sun zaɓi ‘yan takarar su na zaɓen gwamnan Jihar Kogi, kuma jam’iyyu 17 ne su ka yi hakan a Imo da Bayelsa.

 

Mista Okoye ya tunatar da cewa dukkan jam’iyyun siyasa da za su shiga waɗannan zaɓuɓɓuka guda uku sun cike fom mai lamba EC9 mai ɗauke da cikakkun bayanan ‘yan takara da daftarin rantsuwa a kotu da kuma Fom EC9B mai ɗauke da jerin sunayen ‘yan takarar su.

 

Ya ce: “Kamar yadda sashe na 29 (3) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar, hukumar za ta wallafa sunaye da bayanan ‘yan takarar a ofisoshin ta na hedikwatar jihohin uku da ƙananan hukumomin su a ranar Juma’a, 12 ga Mayu, 2023.

 

“Mu na kira ga ‘yan Nijeriya da su karanta bayanan da kyau. Musamman mu na so duk wani ɗan takara da ya shiga zaɓen fidda gwani na jam’iyyar idan ya ga wani bayani da ya tabbatar na ƙarya ne da wani ɗan takara ya bayar, ya na iya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya kamar yadda sashe na 29(5) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Jami’an Kasashen Sin Da Amurka Sun Tattauna Game Da Alakar Kasashen Biyu

Next Post

Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Related

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

52 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

6 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

7 hours ago
Next Post
Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.