ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo

by Sulaiman
3 years ago
Inec

A ranar Juma’a, 12 ga Mayu, 2023 Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta kafe sunayen ‘yan takarar da za su fafata a zaɓuɓɓukan gwamna na cike girbi da za a yi a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi.

 

Hukumar ta yi kira ga jama’a da su yi wa sunayen karatun ta-natsu domin gano idan wani ɗan takara ya ba da bayanin bogi game da kan shi domin ɗaukar mataki.

ADVERTISEMENT
  • Ina Kammala Wa’adin Mulkina Na Biyu Zan Yi Ritaya Daga Siyasa – Gwamna Sule

Babban Kwamishina kuma shugaban kwamitin wayar da kan jama’a kan al’amurran zaɓe na INEC, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa ga manema labarai da ya rattaba wa hannu.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

A ranar 25 ga Oktoba, 2022 ne dai hukumar ta fitar da jadawalin ayyuka da tsare-tsaren da za a aiwatar a zaɓuɓɓuka uku na cike gurbi na gwamnonin jihohin waɗanda za a gudanar a ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, 2023.

 

Jam’iyyun siyasa sun gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwani kamar yadda doka ta tanada, kuma sun wallafa sunayen ‘yan takarar su da mataimakan su tare da bayanan su a gidan yanar da hukumar ta tanada domin ɗora irin waɗannan hotunan da bayanan kafin wa’adin karfe 6 na yamma na ranar 5 ga Mayu ya cika.

 

Dukkan jam’iyyu 18 sun zaɓi ‘yan takarar su na zaɓen gwamnan Jihar Kogi, kuma jam’iyyu 17 ne su ka yi hakan a Imo da Bayelsa.

 

Mista Okoye ya tunatar da cewa dukkan jam’iyyun siyasa da za su shiga waɗannan zaɓuɓɓuka guda uku sun cike fom mai lamba EC9 mai ɗauke da cikakkun bayanan ‘yan takara da daftarin rantsuwa a kotu da kuma Fom EC9B mai ɗauke da jerin sunayen ‘yan takarar su.

 

Ya ce: “Kamar yadda sashe na 29 (3) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar, hukumar za ta wallafa sunaye da bayanan ‘yan takarar a ofisoshin ta na hedikwatar jihohin uku da ƙananan hukumomin su a ranar Juma’a, 12 ga Mayu, 2023.

 

“Mu na kira ga ‘yan Nijeriya da su karanta bayanan da kyau. Musamman mu na so duk wani ɗan takara da ya shiga zaɓen fidda gwani na jam’iyyar idan ya ga wani bayani da ya tabbatar na ƙarya ne da wani ɗan takara ya bayar, ya na iya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya kamar yadda sashe na 29(5) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.”

Inec
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Inec
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Inec

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Inec

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.