Yanzu haka ana shirye-shiryen gudanar da taron kasa da kasa na tattauna batutuwan raya tattalin arziki na Davos na yanayin zafi karo na 16, taron da aka fi sani da dandalin Davos. A bana za a gudanar da taron ne tsakanin ranakun Talata 24 zuwa Alhamis 26 ga watan nan na Yuni, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin, bisa taken “sana’o’i a sabon zamani.”
A bana taron zai mayar da hankali ne ga muhimman fannoni biyar, wadanda suka hada da warware batu game da tattalin arzikin duniya, da hange game da kasar Sin, da halin da masana’antun duniya suka fuskanta na taka musu birki, da zuba jari kan al’umma da duniyar bil’adama da batun sabbin makamashi da hajoji.
Game da hakan, jami’i a hukumar tsara manufofin ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin Chen Shuai, ya ce Sin za ta yi amfani da taron na Davos na bana, wajen jaddada aniyarta, ta ci gaba da kwazo don cimma nasarar bude kofa bisa matsayin koli, da rarraba damammakinta na ci gaba da ta samu tare da sauran sassan kasa da kasa.
A nata bangare kuwa, Gim Huay Neo, babbar daraktar dandalin tattalin arziki na duniya, ta shaidawa wani taron menema labarai da ya gudana a baya bayan nan cewa, daya daga cikin yankunan duniya mafiya samun sauye-sauye a duniya shi ne nahiyar Asiya, nahiyar da ke kunshe da kaso 60 bisa dari na ci gaban tattalin arzikin duniya, kuma cikin wannan adadi kasar Sin ita kadai na bayar da gudummawar rabin kason ci gaban nahiyar. Jami’ar ta kara da cewa, dandalin Davos na bana zai samar da zarafi ga mahalartansa, na zurfafa fahimtarsu ga salon ci gaban Sin da sauran sassan Asiya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp