• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa A Watan Nuwamba

by Zubairu M Lawal
1 year ago
in Labarai
0
Za A Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomin Jihar Nasarawa A Watan Nuwamba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Jihar Nasarawa, ta sanar da ranar da za ta gudanar da zaben Kananan Hukumomi a jihar.

Da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa, Shugaban Hukumar, Barista Ayuba Wandai, ya ce za a gudanar da zaben a ranar 2 ga watan Nuwamba, 2024.

  • Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2
  • Ka Da Mu Yanke Kauna Da Nijeriya – Jonathan

Wandai, ya ce; “Wa’adin shugabannin kananan hukumomin da aka zaba a shekarar 2021 ya kare.”

Ya ce dokar zaben kananan hukumomi ta jihar da aka yi wa gyara a 2018 ta ba su damar u yi shekara uku ne a kujerar.

Ya ce sun tattauna da shugabannin jami’yyu da ke jihar kuma sun gamsu da tsare-tsarensu.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Ya ce; sun bayar da damar gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyu daga ranar Juma’a 11 zuwa Alhamis 17 ga watan Oktoba, 2024.

Sanan za a fara gudanar da yakin niman zabe daga ranar 18 ga watan Oktoba.

Haka kuma kowace jam’iyya da ta shiga zaben za ta mika sunayen ‘yan takararta a ranar 29 ga watan Oktoba.

Sannan a gudanar da zaben a ranar 2 ga watan Nuwamba.

Ya ce hukumar za ta sanar da duk sakamakon da ya zo teburrinta.

Cikin takardum ka’idojin zaɓen an sanya kudin sayan fom din takara na Shugabannin Kananan Hukumomi a kan Naira miliyan 2.5.

Na Kansila zai tashi a kan Naira miliyan daya kacal.

Haka zalika za a sauke sunan duk dan takarar da aka same shi a matsayin ma’aikacin Gwamnatin Tarayya ko ta jiha ko ta karamar hukumar da ya tsaya takarar ba tare da ya ajiye aikin ba.

Ya ce masu kada kuri’a za su kasance daga shekara 18 zuwa sama.

Kuma an tanadi matakan tsaro domin gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukumaNasarawaZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2

Next Post

Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Za Ta Kawo Sabbin Damammaki Ga Duniya

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

4 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

5 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

10 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

12 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

13 hours ago
Next Post
Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Za Ta Kawo Sabbin Damammaki Ga Duniya

Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Za Ta Kawo Sabbin Damammaki Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.