• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Kammala Aikin Titin Kano Zuwa Kaduna Da Gadar Neja A Ranar 15 Ga Mayu – Gwamnati

by Sulaiman
3 years ago
Titin Kano

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, a jiya ya ce, ‘yan kwangilar da ke gudanar da aikin hanyoyin Kano zuwa Zariya da na Zariya zuwa Kaduna tare da aikin Gadar Neja na 2 za su kammala tare da mikasu a ranar 15 ga watan Mayun 2023.

Ya shaida hakan ne ga ‘yan jarida bayan kammala zaman Majalisar zantawar ta kasa (FEC), tare da cewa, shi ma aikin babban hanyar Legas zuwa Ibadan mai nisan kilomita 116 tare da manyan gadojinsa zai kammala kuma za a mika wa gwammati shi zuwa ranar 30 ga watan Afrilu.

  • NAHCON Ta Bai Wa Jihohi Wa’adin Awa 48 Da Su Tura Kudaden Aikin Hajjin 2023

Sannan, ya ce, an amince da fitar da naira biliyan 1.39 domin farfado da kwangila da nufin kammala shi na Gadar Uto karo na biyu mai nisan kilomita 2.6 a Ikenje da ke jihar Delta daga naira biliyan 4.435 zuwa biliyan 5.835.

Ya ce, “Aikin Gadar Loko-Oweto tunin aka kammala shi. Shi ma Gadar Ikom an kammala. Sakatariyar Gwamnatin tarayya a jihohin Nasarawa, Bayelsa da Zamfara da na Awka an kammalasu su din ma, kazalika, rukunin gidajen Zuba, da gidaje 700 sun zama a kimtse ko yanzu za a iya kaddamar da su,” ya kara da cewa.

Shi kuma ministan noma da raya karkara, Muhammad Abubakar, ya ce, bukatar gina shalkwatar ma’aikatar noma da bunkasa yankunan karkara na gwamnatin tarayya ya samu amincewa.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

A cewarsa, ana son a karon farko za a kashe naira biliyan 6 domin fara gudanar da aikin sabuwar Shalkwatar.

Abubakar ya ce, an tsara cewa ginin Shalkwatar mai hawa 10 za a kirasa da suna gidan noma.

Dangane da hauhawar farashin shinkafa, ya ce ana yin abubuwa da yawa don tabbatar da samun shinkafar da tabbatar da wadatuwarsa a cikin kasa, don kara rage farashinsa da saukinsa “Tun da Nijeriya ce ta daya a nahiyar Afirka wajen noman shinkafa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 
Labarai

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
Next Post
Yanzu-yanzu: Sojoji Sun Yi Watsi Da Kaloli 53, Sun Fitar Da Sabbi 28 A Abuja

Yanzu-yanzu: Sojoji Sun Yi Watsi Da Kaloli 53, Sun Fitar Da Sabbi 28 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.