Kafin shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron koli na kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na 2 a birnin Astana na kasar Kazakhstan, za a watsa shirin “Bayanan magabata dake jan hankalin Xi Jinping” a kafofin watsa shirye-shirye da dama na kasashen biyar, shirin da kafar CMG ta kasar Sin ta tsara shi.
Ana sa ran watsa shirin tun daga ranar Litinin 16 ga watan nan a kasashen Kazakhstan, da Kyrgyzstan, da Tajikistan, da Turkmenistan da kuma Uzbekistan.
Rahotanni na cewa, a ‘yan kwanakin baya-bayan nan, kafofin watsa shirye-shirye da dama dake kasashen Asiya da Turai, sun gudanar da gwajin watsa shirin, wanda sassa daban daban ke ta doki, da dakon zuwan lokacin nuna cikakkensa. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp