• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ‘Yantar Da Falasɗinawa Nan Ba Da Jimawa Ba – Fani-Kayode

by Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama Femi Fani-Kayode, ya bayyana fatansa na ganin cewa, nan ba da jimawa ba an kawo karshen kisan kiyashin da ake ci gaba da yi a Gaza da kuma take hakkin bil adama da Sojojin Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.

 

Mista Fani-Kayode, wanda ya bayyana hakan a ranar Litinin din da ta gabata a yayin bikin ranar Aqsa na 2024 da kungiyar wayar da kan musulmi ta kasa da kasa ta shirya a Legas, ya danganta fatansa kan yadda duniya ke nuna bacin rai da ya biyo bayan kisan kiyashin.

  • Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Matsawa Isra’ila Ta Dakatar Da Ayyukan Soji A Gaza
  • Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

A cewar rahotanni, an kashe mutane fiye da 40,000 da suka hada da mata da yara a yakin da ake ci gaba da gwabzawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Ya ce: “Wajibi ne a kan mu da duk mutum mai hankali ya yi magana kan wannan barnar ta asarar rayukan al’umma.

 

“Kuma na yi farin ciki cewa, zanga-zangar adawa da mugun aikin Isra’ila tana faruwa a duk faɗin duniya a yau. Tana faruwa a Amurka. Tana faruwa a Turai. Afirka ta Kudu ce ke kan gaba a nahiyar Afirka, kuma mutane da yawa suna tofa albarkacin bakinsu.

 

“Ireland ta yi Allah wadai da hakan. Belgium ta yi Allah wadai da hakan. Spain ta yi Allah wadai da hakan. Kashi 90 cikin 100 na kasashen Kudancin Amurka sun yi Allah wadai da hakan. Mutane da dama a cikin Faransa sun yi Allah wadai da hakan. Hatta Birtaniya ta rage sayar wa Isra’ila da makamai.

 

“Duniya duka tana yin Allah wadai da aikin Isra’ila. Manyan cibiyoyin karatu a Amurka, kamar Harvard, Yale, Oxford, da Cambridge, sun yi zanga-zangar adawa da abin da ke faruwa a Gaza.

 

“Yadda muke fada, da yadda muke magana kan abin da ke faruwa a Gaza a yau, shi ne irin yadda mutane suka yaki wariyar launin fata a Afirka ta Kudu wanda hakan ya bai wa kasar ‘yanci. Don haka, lokaci ne kadan ya rage al’ummar Falasɗinawa su samu ‘yanci na gaskiya.

 

“Muna yin furucin adawa da aikin Isra’ila a nan ta hanyar yin magana a kullum a kasarmu Nijeriya. Dan adam, a ko ina yake Dan Adam ne, Babu ruwanmu da banbancin addini.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaIsra'ilaLebanon
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wane Irin Hadin Kai Ne Afirka Ke Bukata?

Next Post

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

4 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

6 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

7 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

17 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

18 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

24 hours ago
Next Post
Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Jaridar New York Times: Sin Ta Mamaye Ci Gaban Duniya Na Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.