• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau na ga wannan labari: Charles Onunaiju, wani masanin ilimin huldar kasa da kasa na Najeriya, ya ce asusun tarayyar Amurka na ci gaba da kara kudin ruwa, matakin da ke iya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa.

Don neman shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki, asusun tarayyar Amurka ya kara kudin ruwa har sau 6, tun farkon shekarar 2022.

  • Sin: Gaskiya Ba Ta Buya, Kuma Adalci Yana Bayyana Kansa

Amma me ya sa matakin ya shafi sauran kasashe? Saboda wannan manufar za ta janyo dalar Amurka daga kasuwannin kasa da kasa, don su koma kasar Amurka. Hakan kuma zai sa a dinga canza kudaden sauran kasashe zuwa dalar Amurka, lamarin da zai haddasa faduwar darajar kudaden, da hauhawar farashin kayayyaki a wadannan kasashe, da karancin dalar Amurka, da jarin waje a kasuwanninsu, gami da raguwar adadin kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje.

Don tinkarar wannan mummunan tasiri, manyan bankunan sauran kasashe su ma sun daga kudin ruwa don neman kiyaye dalar Amurka a gida. Misali, babban bankin Najeriya ya riga ya daga kudin ruwa zuwa 16.5%. Sai dai manufar ba ta yi amfani sosai ba, ganin yadda darajar Naira na ci gaba da raguwa. A sa’i daya kuma, karuwar kudin ruwa na haifar da karin matsin lamba ga kamfanonin da suka ci bashi daga bankuna.

A cewar Charles Onunaiju, yanzu Nijeriya na fama da hauhawar farashin kayayyaki da matsalar karancin dalar Amurka a kasuwa, da faduwar darajar kudin kasar da dai sauransu, galibi saboda yadda take fuskantar matsin lamba daga wasu manufofin kasashen ketare. Kana Najeriya da sauran kasashe masu tasowa na fuskantar matsalolin raguwar guraben aikin yi, da karuwar bashin da ake ci. Ta wata manufarta kadai, kasar Amurka ta tura matsalolin hauhawar farashin kayayyaki, da koma bayan tattalin arziki, ga sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Matakan “kashin dankali” mai kama da wannan, da kasar Amurka ta yi wa sauran kasashe, sun yi yawa. Idan har mun dauki aminan kasar Amurka, wato kasashen Turai a matsayin misali. Ta hanyar fakewa da maganar daidaita yanayin da ake ciki a nahiyar Turai a fannin tsaro, kasar Amurka ta mai da kasashen Turai karkashin jagorancinta. Kana ta yi amfani da matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fuskanta wajen sayar musu da iskar gas mai tsada matuka. Ban da wannan kuma, kasar Amurka ta ba da dimbin tallafi ga sana’ar kirkiro motoci masu amfani da lantarki ta kasar, don janyo masana’antun Turai zuwa gidanta. Ga shi, kasar ba ta kyautatawa aminanta, balle ma sauran kasashe.

A wannan zamanin da muke ciki, wata kasa kadai take samun dimbin tallafi daga kasar Amurka, wato kasar Ukraine. Amma dalilin da ya sa haka, shi ne Amurka na yin amfani da Ukraine wajen raunana kasar Rasha. An biya kudi, don sanya mutanen kasar Ukraine, maimakon na kasar Amurka zub da jini. Gaskiya Amurkawa suna da wayo.

Shafin yanar gizo ta Internet ta Modern Diplomacy, na Turai, ya ce kasar Amurka kasa ce dake son kwatar dukiyoyi daga sauran kasashe. Ko da yake wata babbar kasa ce, amma za ka yarda da manufarta ta “kashin dankali”?(Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mata Da Yara Akalla 721 Aka Yi Wa Fyade Cikin Watanni 9 A Kano

Next Post

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

16 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

18 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

19 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

20 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.