• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

by CMG Hausa
3 years ago
FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

Yau na ga wannan labari: Charles Onunaiju, wani masanin ilimin huldar kasa da kasa na Najeriya, ya ce asusun tarayyar Amurka na ci gaba da kara kudin ruwa, matakin da ke iya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa.

Don neman shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki, asusun tarayyar Amurka ya kara kudin ruwa har sau 6, tun farkon shekarar 2022.

  • Sin: Gaskiya Ba Ta Buya, Kuma Adalci Yana Bayyana Kansa

Amma me ya sa matakin ya shafi sauran kasashe? Saboda wannan manufar za ta janyo dalar Amurka daga kasuwannin kasa da kasa, don su koma kasar Amurka. Hakan kuma zai sa a dinga canza kudaden sauran kasashe zuwa dalar Amurka, lamarin da zai haddasa faduwar darajar kudaden, da hauhawar farashin kayayyaki a wadannan kasashe, da karancin dalar Amurka, da jarin waje a kasuwanninsu, gami da raguwar adadin kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje.

Don tinkarar wannan mummunan tasiri, manyan bankunan sauran kasashe su ma sun daga kudin ruwa don neman kiyaye dalar Amurka a gida. Misali, babban bankin Najeriya ya riga ya daga kudin ruwa zuwa 16.5%. Sai dai manufar ba ta yi amfani sosai ba, ganin yadda darajar Naira na ci gaba da raguwa. A sa’i daya kuma, karuwar kudin ruwa na haifar da karin matsin lamba ga kamfanonin da suka ci bashi daga bankuna.

A cewar Charles Onunaiju, yanzu Nijeriya na fama da hauhawar farashin kayayyaki da matsalar karancin dalar Amurka a kasuwa, da faduwar darajar kudin kasar da dai sauransu, galibi saboda yadda take fuskantar matsin lamba daga wasu manufofin kasashen ketare. Kana Najeriya da sauran kasashe masu tasowa na fuskantar matsalolin raguwar guraben aikin yi, da karuwar bashin da ake ci. Ta wata manufarta kadai, kasar Amurka ta tura matsalolin hauhawar farashin kayayyaki, da koma bayan tattalin arziki, ga sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Matakan “kashin dankali” mai kama da wannan, da kasar Amurka ta yi wa sauran kasashe, sun yi yawa. Idan har mun dauki aminan kasar Amurka, wato kasashen Turai a matsayin misali. Ta hanyar fakewa da maganar daidaita yanayin da ake ciki a nahiyar Turai a fannin tsaro, kasar Amurka ta mai da kasashen Turai karkashin jagorancinta. Kana ta yi amfani da matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fuskanta wajen sayar musu da iskar gas mai tsada matuka. Ban da wannan kuma, kasar Amurka ta ba da dimbin tallafi ga sana’ar kirkiro motoci masu amfani da lantarki ta kasar, don janyo masana’antun Turai zuwa gidanta. Ga shi, kasar ba ta kyautatawa aminanta, balle ma sauran kasashe.

A wannan zamanin da muke ciki, wata kasa kadai take samun dimbin tallafi daga kasar Amurka, wato kasar Ukraine. Amma dalilin da ya sa haka, shi ne Amurka na yin amfani da Ukraine wajen raunana kasar Rasha. An biya kudi, don sanya mutanen kasar Ukraine, maimakon na kasar Amurka zub da jini. Gaskiya Amurkawa suna da wayo.

Shafin yanar gizo ta Internet ta Modern Diplomacy, na Turai, ya ce kasar Amurka kasa ce dake son kwatar dukiyoyi daga sauran kasashe. Ko da yake wata babbar kasa ce, amma za ka yarda da manufarta ta “kashin dankali”?(Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.