• Leadership Hausa
Sunday, February 5, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

Yau na ga wannan labari: Charles Onunaiju, wani masanin ilimin huldar kasa da kasa na Najeriya, ya ce asusun tarayyar Amurka na ci gaba da kara kudin ruwa, matakin da ke iya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa.

Don neman shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki, asusun tarayyar Amurka ya kara kudin ruwa har sau 6, tun farkon shekarar 2022.

  • Sin: Gaskiya Ba Ta Buya, Kuma Adalci Yana Bayyana Kansa

Amma me ya sa matakin ya shafi sauran kasashe? Saboda wannan manufar za ta janyo dalar Amurka daga kasuwannin kasa da kasa, don su koma kasar Amurka. Hakan kuma zai sa a dinga canza kudaden sauran kasashe zuwa dalar Amurka, lamarin da zai haddasa faduwar darajar kudaden, da hauhawar farashin kayayyaki a wadannan kasashe, da karancin dalar Amurka, da jarin waje a kasuwanninsu, gami da raguwar adadin kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje.

Don tinkarar wannan mummunan tasiri, manyan bankunan sauran kasashe su ma sun daga kudin ruwa don neman kiyaye dalar Amurka a gida. Misali, babban bankin Najeriya ya riga ya daga kudin ruwa zuwa 16.5%. Sai dai manufar ba ta yi amfani sosai ba, ganin yadda darajar Naira na ci gaba da raguwa. A sa’i daya kuma, karuwar kudin ruwa na haifar da karin matsin lamba ga kamfanonin da suka ci bashi daga bankuna.

A cewar Charles Onunaiju, yanzu Nijeriya na fama da hauhawar farashin kayayyaki da matsalar karancin dalar Amurka a kasuwa, da faduwar darajar kudin kasar da dai sauransu, galibi saboda yadda take fuskantar matsin lamba daga wasu manufofin kasashen ketare. Kana Najeriya da sauran kasashe masu tasowa na fuskantar matsalolin raguwar guraben aikin yi, da karuwar bashin da ake ci. Ta wata manufarta kadai, kasar Amurka ta tura matsalolin hauhawar farashin kayayyaki, da koma bayan tattalin arziki, ga sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa.

Labarai Masu Nasaba

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

Matakan “kashin dankali” mai kama da wannan, da kasar Amurka ta yi wa sauran kasashe, sun yi yawa. Idan har mun dauki aminan kasar Amurka, wato kasashen Turai a matsayin misali. Ta hanyar fakewa da maganar daidaita yanayin da ake ciki a nahiyar Turai a fannin tsaro, kasar Amurka ta mai da kasashen Turai karkashin jagorancinta. Kana ta yi amfani da matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fuskanta wajen sayar musu da iskar gas mai tsada matuka. Ban da wannan kuma, kasar Amurka ta ba da dimbin tallafi ga sana’ar kirkiro motoci masu amfani da lantarki ta kasar, don janyo masana’antun Turai zuwa gidanta. Ga shi, kasar ba ta kyautatawa aminanta, balle ma sauran kasashe.

A wannan zamanin da muke ciki, wata kasa kadai take samun dimbin tallafi daga kasar Amurka, wato kasar Ukraine. Amma dalilin da ya sa haka, shi ne Amurka na yin amfani da Ukraine wajen raunana kasar Rasha. An biya kudi, don sanya mutanen kasar Ukraine, maimakon na kasar Amurka zub da jini. Gaskiya Amurkawa suna da wayo.

Shafin yanar gizo ta Internet ta Modern Diplomacy, na Turai, ya ce kasar Amurka kasa ce dake son kwatar dukiyoyi daga sauran kasashe. Ko da yake wata babbar kasa ce, amma za ka yarda da manufarta ta “kashin dankali”?(Bello Wang)

Previous Post

Mata Da Yara Akalla 721 Aka Yi Wa Fyade Cikin Watanni 9 A Kano

Next Post

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

Related

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

10 hours ago
Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

11 hours ago
Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

12 hours ago
Amurka Ba Ta Cancanci Sukar Kasar Sin Ba
Daga Birnin Sin

Amurka Ba Ta Cancanci Sukar Kasar Sin Ba

23 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Cika Alkawarin Ta Tare Da Yin Abun Da Ya Dace Kan Muhimman Batutuwa

1 day ago
Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Amurka Ta Nuna Girmamawa Yayin Sake Bude Ofishin Jakadancinta A Solomon

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

February 4, 2023
Gwamnatin Katsina Za Ta Yi Bincike Kan Kisan Da ‘Yan Bindiga Suka Yi Wa Mutum 41

Gwamnatin Katsina Za Ta Yi Bincike Kan Kisan Da ‘Yan Bindiga Suka Yi Wa Mutum 41

February 4, 2023
An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

An Gabatar Da Shirin Tallata Bikin Fitilu Na Gargajiyar Sin A Afrika Ta Kudu Da Habasha

February 4, 2023
Kashu

Nijeriya Na Samun Fiye Da Dala Miliyan 250 Daga Kashun Da Ake Fitarwa Waje -Minista

February 4, 2023
Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

Sin Za Ta Hada Hannu Da MDD Wajen Shawo Kan Kalubalen Duniya

February 4, 2023
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

February 4, 2023
Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

Wang Yi: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Rika Tuntubar Juna Domin Kaucewa Rashin Fahimta

February 4, 2023
Tinubu Yana Kaunar Nijeriya, Ku Zabe Shi – Buhari Ga ‘Yan Nijeriya

Tinubu Yana Kaunar Nijeriya, Ku Zabe Shi – Buhari Ga ‘Yan Nijeriya

February 4, 2023
Rashin Adalci Tsakanin ‘Ya’ya Yana Jawo Fitintinu (Fatawa)

Rashin Adalci Tsakanin ‘Ya’ya Yana Jawo Fitintinu (Fatawa)

February 4, 2023
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

February 4, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.