ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Ka Yarda Da Manufar “Kashin Dankali”?

by CMG Hausa
4 years ago
FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

FILE - Pedestrians shop at a street market in Lagos, Nigeria, on Sept. 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba, File)

Yau na ga wannan labari: Charles Onunaiju, wani masanin ilimin huldar kasa da kasa na Najeriya, ya ce asusun tarayyar Amurka na ci gaba da kara kudin ruwa, matakin da ke iya haifar da mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa.

Don neman shawo kan matsalar hauhawar farashin kayayyaki, asusun tarayyar Amurka ya kara kudin ruwa har sau 6, tun farkon shekarar 2022.

  • Sin: Gaskiya Ba Ta Buya, Kuma Adalci Yana Bayyana Kansa

Amma me ya sa matakin ya shafi sauran kasashe? Saboda wannan manufar za ta janyo dalar Amurka daga kasuwannin kasa da kasa, don su koma kasar Amurka. Hakan kuma zai sa a dinga canza kudaden sauran kasashe zuwa dalar Amurka, lamarin da zai haddasa faduwar darajar kudaden, da hauhawar farashin kayayyaki a wadannan kasashe, da karancin dalar Amurka, da jarin waje a kasuwanninsu, gami da raguwar adadin kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasashen waje.

ADVERTISEMENT

Don tinkarar wannan mummunan tasiri, manyan bankunan sauran kasashe su ma sun daga kudin ruwa don neman kiyaye dalar Amurka a gida. Misali, babban bankin Najeriya ya riga ya daga kudin ruwa zuwa 16.5%. Sai dai manufar ba ta yi amfani sosai ba, ganin yadda darajar Naira na ci gaba da raguwa. A sa’i daya kuma, karuwar kudin ruwa na haifar da karin matsin lamba ga kamfanonin da suka ci bashi daga bankuna.

A cewar Charles Onunaiju, yanzu Nijeriya na fama da hauhawar farashin kayayyaki da matsalar karancin dalar Amurka a kasuwa, da faduwar darajar kudin kasar da dai sauransu, galibi saboda yadda take fuskantar matsin lamba daga wasu manufofin kasashen ketare. Kana Najeriya da sauran kasashe masu tasowa na fuskantar matsalolin raguwar guraben aikin yi, da karuwar bashin da ake ci. Ta wata manufarta kadai, kasar Amurka ta tura matsalolin hauhawar farashin kayayyaki, da koma bayan tattalin arziki, ga sauran kasashe, musamman ma kasashe masu tasowa.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Matakan “kashin dankali” mai kama da wannan, da kasar Amurka ta yi wa sauran kasashe, sun yi yawa. Idan har mun dauki aminan kasar Amurka, wato kasashen Turai a matsayin misali. Ta hanyar fakewa da maganar daidaita yanayin da ake ciki a nahiyar Turai a fannin tsaro, kasar Amurka ta mai da kasashen Turai karkashin jagorancinta. Kana ta yi amfani da matsalar karancin makamashin da kasashen Turai suke fuskanta wajen sayar musu da iskar gas mai tsada matuka. Ban da wannan kuma, kasar Amurka ta ba da dimbin tallafi ga sana’ar kirkiro motoci masu amfani da lantarki ta kasar, don janyo masana’antun Turai zuwa gidanta. Ga shi, kasar ba ta kyautatawa aminanta, balle ma sauran kasashe.

A wannan zamanin da muke ciki, wata kasa kadai take samun dimbin tallafi daga kasar Amurka, wato kasar Ukraine. Amma dalilin da ya sa haka, shi ne Amurka na yin amfani da Ukraine wajen raunana kasar Rasha. An biya kudi, don sanya mutanen kasar Ukraine, maimakon na kasar Amurka zub da jini. Gaskiya Amurkawa suna da wayo.

Shafin yanar gizo ta Internet ta Modern Diplomacy, na Turai, ya ce kasar Amurka kasa ce dake son kwatar dukiyoyi daga sauran kasashe. Ko da yake wata babbar kasa ce, amma za ka yarda da manufarta ta “kashin dankali”?(Bello Wang)

Adalci
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Dauki Karin Masu Share Tituna Don Tsaftace Muhalli

Ganduje Ya Amince Da Kammala Titin Garin Kwankwaso Da Sauran Wasu Aiyuka A Kano

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.