• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ƙalubalanci Ƙarin Kuɗin Kira Da Data A Kotu – NATCOMS  

by Naziru Adam Ibrahim and Sulaiman
9 months ago
NATCOMS

A ranar Litinin ne gwamnatin Nijeriya ta hannun hukumar sadarwa ta (NCC) ta duba koken kamfanonin sadarwar, inda ta amince musu da su yi ƙarin kuɗin kira da sayen data da kashi 50 cikin 100 sabanin abinda suka bukata.

 

A kwanakin nan Kamfanonin sadarwa a Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar gudanarwar kamfanin MTN, Karl Toriola, sun buƙaci amincewar gwamnatin tarayya kan su yi ƙarin kashi 100 bisa 100 na kuɗin kiran waya da data.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Dalilinsu na neman wannan ƙarin, shi ne tsadar rayuwa, wanda ya ce kamfanin sadarwa a Nijeriya na fuskantar barazanar durƙushewa a sakamakon yadda farashin komai ya yi tashin gauron-zabi kama daga farashin man fetur da farashin kuɗin wuta da sauransu.

 

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

A cewar Karl Toriola, a halin yanzu ba batun riba suke ba, sai dai yadda za su ci gaba da kasuwanci, ko a kwanakin baya kungiyar kamfanonin sadarwa ta yi barazanar za a iya samun katsewar sabis ɗin waya a wasu sassa na ƙasar muddin ƙarin bai tabbata ba.

 

Hakan na nufin za a iya samun tangarɗa a fannoni daban-daban da suka shafi tsaro da kiwon lafiya da ilimi da harkokin kasuwanci da sauran al’amuran yau da kullum, kasancewar irin tasirin da kafafen sadarwa ke da shi a rayuwar al’umma.

 

Wannan ta ƙaddamar ƙarin dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa game da hauhawar farashi a sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnatin Nijeriya, wanda ake alaƙanta su da cire tallafin man fetur.

 

Shugaban ƙungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta NATCOMS, Deolu Ogunbanjo, ya ce hukumar NCC ba ta tuntuɓesu ba game da ƙarin kashi 50 ciki 100 na farashin kuɗin waya da datan da ta yi.

 

A cewarsa suna sane da ƙalubalen da kamfanonin sadarwa ke fuskanta, tare da bayar da shawarar ƙarin kashi 5 ko 10 cikin 100, ya kuma shaida cewa matakin NCC na ƙarin abu ne da ba za su lamunta ba, inda ya sha alwashin ƙalubalantar ƙarin ƙudin a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja
Labarai

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi
Manyan Labarai

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Next Post
Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025
Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

October 22, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025
Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.