ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ƙalubalanci Ƙarin Kuɗin Kira Da Data A Kotu – NATCOMS  

by Naziru Adam Ibrahim and Sulaiman
10 months ago
NATCOMS

A ranar Litinin ne gwamnatin Nijeriya ta hannun hukumar sadarwa ta (NCC) ta duba koken kamfanonin sadarwar, inda ta amince musu da su yi ƙarin kuɗin kira da sayen data da kashi 50 cikin 100 sabanin abinda suka bukata.

 

A kwanakin nan Kamfanonin sadarwa a Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar gudanarwar kamfanin MTN, Karl Toriola, sun buƙaci amincewar gwamnatin tarayya kan su yi ƙarin kashi 100 bisa 100 na kuɗin kiran waya da data.

ADVERTISEMENT
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Dalilinsu na neman wannan ƙarin, shi ne tsadar rayuwa, wanda ya ce kamfanin sadarwa a Nijeriya na fuskantar barazanar durƙushewa a sakamakon yadda farashin komai ya yi tashin gauron-zabi kama daga farashin man fetur da farashin kuɗin wuta da sauransu.

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

A cewar Karl Toriola, a halin yanzu ba batun riba suke ba, sai dai yadda za su ci gaba da kasuwanci, ko a kwanakin baya kungiyar kamfanonin sadarwa ta yi barazanar za a iya samun katsewar sabis ɗin waya a wasu sassa na ƙasar muddin ƙarin bai tabbata ba.

 

Hakan na nufin za a iya samun tangarɗa a fannoni daban-daban da suka shafi tsaro da kiwon lafiya da ilimi da harkokin kasuwanci da sauran al’amuran yau da kullum, kasancewar irin tasirin da kafafen sadarwa ke da shi a rayuwar al’umma.

 

Wannan ta ƙaddamar ƙarin dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa game da hauhawar farashi a sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnatin Nijeriya, wanda ake alaƙanta su da cire tallafin man fetur.

 

Shugaban ƙungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta NATCOMS, Deolu Ogunbanjo, ya ce hukumar NCC ba ta tuntuɓesu ba game da ƙarin kashi 50 ciki 100 na farashin kuɗin waya da datan da ta yi.

 

A cewarsa suna sane da ƙalubalen da kamfanonin sadarwa ke fuskanta, tare da bayar da shawarar ƙarin kashi 5 ko 10 cikin 100, ya kuma shaida cewa matakin NCC na ƙarin abu ne da ba za su lamunta ba, inda ya sha alwashin ƙalubalantar ƙarin ƙudin a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.