• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ƙalubalanci Ƙarin Kuɗin Kira Da Data A Kotu – NATCOMS  

by Naziru Adam Ibrahim and Sulaiman
10 months ago
NATCOMS

A ranar Litinin ne gwamnatin Nijeriya ta hannun hukumar sadarwa ta (NCC) ta duba koken kamfanonin sadarwar, inda ta amince musu da su yi ƙarin kuɗin kira da sayen data da kashi 50 cikin 100 sabanin abinda suka bukata.

 

A kwanakin nan Kamfanonin sadarwa a Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar gudanarwar kamfanin MTN, Karl Toriola, sun buƙaci amincewar gwamnatin tarayya kan su yi ƙarin kashi 100 bisa 100 na kuɗin kiran waya da data.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Dalilinsu na neman wannan ƙarin, shi ne tsadar rayuwa, wanda ya ce kamfanin sadarwa a Nijeriya na fuskantar barazanar durƙushewa a sakamakon yadda farashin komai ya yi tashin gauron-zabi kama daga farashin man fetur da farashin kuɗin wuta da sauransu.

 

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

A cewar Karl Toriola, a halin yanzu ba batun riba suke ba, sai dai yadda za su ci gaba da kasuwanci, ko a kwanakin baya kungiyar kamfanonin sadarwa ta yi barazanar za a iya samun katsewar sabis ɗin waya a wasu sassa na ƙasar muddin ƙarin bai tabbata ba.

 

Hakan na nufin za a iya samun tangarɗa a fannoni daban-daban da suka shafi tsaro da kiwon lafiya da ilimi da harkokin kasuwanci da sauran al’amuran yau da kullum, kasancewar irin tasirin da kafafen sadarwa ke da shi a rayuwar al’umma.

 

Wannan ta ƙaddamar ƙarin dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa game da hauhawar farashi a sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnatin Nijeriya, wanda ake alaƙanta su da cire tallafin man fetur.

 

Shugaban ƙungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta NATCOMS, Deolu Ogunbanjo, ya ce hukumar NCC ba ta tuntuɓesu ba game da ƙarin kashi 50 ciki 100 na farashin kuɗin waya da datan da ta yi.

 

A cewarsa suna sane da ƙalubalen da kamfanonin sadarwa ke fuskanta, tare da bayar da shawarar ƙarin kashi 5 ko 10 cikin 100, ya kuma shaida cewa matakin NCC na ƙarin abu ne da ba za su lamunta ba, inda ya sha alwashin ƙalubalantar ƙarin ƙudin a gaban kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

Sashen Masana’Antun Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Ci Gaba Da Zama Kan Gaba a Duniya Cikin Shekaru 15 A Jere

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.