• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe 1m Kowane – Bala Mohammed

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Iyalan

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya shelanta cewa daga yanzu duk wani mutumin da ‘yan bindiga suka kashe a jihar za a bai wa iyalansa tallafin Naira miliyan daya, idan mace ce ko karamin yaro za a ba su Naira 500,000.

Kazalika, wannan tallafin a cewar gwamnan zai shafi dukkanin wani jami’in tsaron da ya rasa ransa a fagen fafatawa da masu garkuwa da mutane.

  • Kisan Lauya: Gwamnan Legas Ya Gana Da Sufeton ‘Yansanda
  • Zan Fi Mayar Da Hankali Kan Ilimi Da Matasa – Kwankwaso

Bala, ya shaida hakan ne a lokacin da ke jawabi a fadar hakimin kasar Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri a wata ziyarar jajanta wa al’ummar yankin da ‘yan bindiga suka kashe mutane sama da 20 a baya-bayan nan.

Ya ce, “Kuma daga yanzu saboda da tausayawa duk wanda ya rasa ransa a Jihar Bauchi, za a bai wa iyalansa miliyan daya, idan mace ce za a ba ta dubu dari 500, idan yaro ne dubu dari 500.

“Wannan tallafi ne bai isa diyya ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

“Mun rasa mutane a nan, mun rasa mutane a Toro mun kuma rasa mutane a sauran wurare; ga shugaban karamar hukumar za mu kidaya mutanen da suka rasu mu yi kokari mu ba su tallafi, saboda masu kawo abinci su suka rasu.

“Sannan da sauran jami’an tsaro da suka rasa rayukansu su ma za mu basu wannan tallafin da ‘yansanda kuma da ‘yan banga.

“Saboda haka ku fito yi ts ranku, ku fito ku yi yaki, mu ba a sanmu a ragonta ba. Ba wai daga Zamfara mutum ya zo ba, ko daga birnin Sin yake ba za mu bar shi ba.

“Muna rokon shugaban ‘yan sanda ya gina mana ofishin’yansanda a wannan garin, mu za mu gina shi kuma ya turo muku ‘yansanda.

“Amma kun san idan babu hanya ba zai ji dadin aiki ba, don haka muna tunanin yadda za a samar da hanyoyi kuma in sha Allahu za a yi.

“A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Bauchi, na zo nan ne domin na jajanta muku bisa kashe mutane da aka yi da kone gidaje da ‘yan bindiga suka yi, Allah ya ba da hakuri, Allah ya ba da hakuri.

“Duk Wani dan bindiga da kuka gani a yankunku ku kashe shi. Na nada wannan umarnin kuma babu wata yafiya. Ba za mu bari mu ci gaba da asarar mutanenmu haka nan ba.

A kwanakin baya ne mahara suka kai hari yankin Alkaleri s jihar, inda suka kashe sama da mutum 20.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
An Fara Ginin Katafariyar Tashar Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana Da Kafin Iska A Arewacin Kasar Sin

An Fara Ginin Katafariyar Tashar Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana Da Kafin Iska A Arewacin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version