ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe 1m Kowane – Bala Mohammed

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Iyalan

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya shelanta cewa daga yanzu duk wani mutumin da ‘yan bindiga suka kashe a jihar za a bai wa iyalansa tallafin Naira miliyan daya, idan mace ce ko karamin yaro za a ba su Naira 500,000.

Kazalika, wannan tallafin a cewar gwamnan zai shafi dukkanin wani jami’in tsaron da ya rasa ransa a fagen fafatawa da masu garkuwa da mutane.

  • Kisan Lauya: Gwamnan Legas Ya Gana Da Sufeton ‘Yansanda
  • Zan Fi Mayar Da Hankali Kan Ilimi Da Matasa – Kwankwaso

Bala, ya shaida hakan ne a lokacin da ke jawabi a fadar hakimin kasar Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri a wata ziyarar jajanta wa al’ummar yankin da ‘yan bindiga suka kashe mutane sama da 20 a baya-bayan nan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Kuma daga yanzu saboda da tausayawa duk wanda ya rasa ransa a Jihar Bauchi, za a bai wa iyalansa miliyan daya, idan mace ce za a ba ta dubu dari 500, idan yaro ne dubu dari 500.

“Wannan tallafi ne bai isa diyya ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Mun rasa mutane a nan, mun rasa mutane a Toro mun kuma rasa mutane a sauran wurare; ga shugaban karamar hukumar za mu kidaya mutanen da suka rasu mu yi kokari mu ba su tallafi, saboda masu kawo abinci su suka rasu.

“Sannan da sauran jami’an tsaro da suka rasa rayukansu su ma za mu basu wannan tallafin da ‘yansanda kuma da ‘yan banga.

“Saboda haka ku fito yi ts ranku, ku fito ku yi yaki, mu ba a sanmu a ragonta ba. Ba wai daga Zamfara mutum ya zo ba, ko daga birnin Sin yake ba za mu bar shi ba.

“Muna rokon shugaban ‘yan sanda ya gina mana ofishin’yansanda a wannan garin, mu za mu gina shi kuma ya turo muku ‘yansanda.

“Amma kun san idan babu hanya ba zai ji dadin aiki ba, don haka muna tunanin yadda za a samar da hanyoyi kuma in sha Allahu za a yi.

“A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Bauchi, na zo nan ne domin na jajanta muku bisa kashe mutane da aka yi da kone gidaje da ‘yan bindiga suka yi, Allah ya ba da hakuri, Allah ya ba da hakuri.

“Duk Wani dan bindiga da kuka gani a yankunku ku kashe shi. Na nada wannan umarnin kuma babu wata yafiya. Ba za mu bari mu ci gaba da asarar mutanenmu haka nan ba.

A kwanakin baya ne mahara suka kai hari yankin Alkaleri s jihar, inda suka kashe sama da mutum 20.

Iyalan
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
An Fara Ginin Katafariyar Tashar Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana Da Kafin Iska A Arewacin Kasar Sin

An Fara Ginin Katafariyar Tashar Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana Da Kafin Iska A Arewacin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.