• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar

by Khalid Idris Doya
9 months ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Injiniya Abubakar Ibrahim Musa matashi ne a Jihar Bauchi da ke arewacin Nijeriya, wanda ya kware wajen hada Sola Panels, wato faranti mai amfani da haske rana ya mayar da shi zuwa lantarki da sauran abubuwan kere-kere, ya shaida cewar ta hanyar kera Farantin nan za a iya samar wa dubban ‘yan Nijeriya ayyukan yi.

Abubakar wanda ke da mallakin kamfanin Kuantun Engineering DPS da ke Jihar Bauchi sun kware a bangaren kere-keren abubuwan da suka shafi na solar Panels da sauran abubuwan da ake sarrafa su domin bayar da wutar lantarki daga hasken rana.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan $1.5 Sakamakon Yin Bahaya A Fili

Injiniya Abubakar Ibrahim Musa da aka haifa a 1982 ya shaida cewar ya karanci ilimin fasaha a bangaren injiniyanci na hada kayan wuta wanda ya samu shaidar matakin karatun digiri na biyu yanzu na neman ya uku.

A binciken da wakilinmu ya gudanar kamfanin na kuma horas da matasa da dama kan harkokin da suka shafi injiniyanci na electrical engineering.

Kamfanin ya kware wajen hada Light Bulbs, Solar Panels, Solar Streetlights, Floodlight, Solar Generators da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Matashin ya ce yana yin kwayayen lantarki da sauran abubuwan da suka shafi lantarki. Ya ce ya hada gwiwwa da wani kawunsa don kirkirar wannnan kamfanin samar da lantarki don tallafa wa al’umma da samar da ayyukan yi ga matasa.

Injiniya Abubakar ya ce wasu kayyakin aikin da suke amfani da su sukan sayo ne daga kasar China, yayin da wasun kuma a Nijeriyar suke samunsu.

Ya ce a kowace rana suna kirkirar solar Panels akalla 60. Ya ce babban kalubalen da yake fuskanta a yanzu shi ne rashin karfin jarin da zai bunkasa kasuwancinsa.

Abubakar ya bayyana cewar sun kirkiri kamfannsu ne lura da yanayin kukan matsin tattalin arziki da ake ciki a kasar nan da kuma rashin aikin yi a tsakanin jama’a.

Ya ce kamfanin nasu suna sarrafa abubuwa da yawa kamar su farantin wuta mai amfani da hasken rana ya maida shi zuwa wutar lantarki (Solar Panel), da kuma yin koyayen hasken wuta na zamani da turakun solar na kan layuka da wasu abubuwa na fasaha.

“Abubuwan da muke sarrafawa kamar shi faranti mai maida hasken rana zuwa wutar lantarki muna samun wasu kayan aikin da muke hadawa wasu kuma saimub shigo da su daga kasar China. Kamar abin da ya shafi Solar Cells da solar ribbon, wires su muna zuwa da sune daga kasar China. Amma irin su

Aluminium profile, glass da sauransu duk muna samu a nan Nijeriya.”

Ya tabbatar da cewar jama’a suna sayen kayansu amma suna bukatar manyan masu sayen da su karfafa musu guiwa wajen sayen abubuwan da suke sarrafawa.

Daga bisani ya yi korafin rashin jari, yana mai cewa harkar da suka shafi Solar suna nan birgik muddin aka dafa lallai za a samu guraben ayyukan yi ga dubban jama’a a Nijeriya da dama da rage dogaro da wutar lantarki a fannoni daban daban.

“Babban burin mu shi ne samar da ayyukan yi a tabbatar ayyuka sun samu a cikin kasa kuma an saukaka wa al’umma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasahaHasken RanaKimiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Bangaren Tsaro Zai Shimfida Yanayi Mai Kyau Ga Bunkasuwar Afirka

Next Post

Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

1 month ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

3 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

3 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

8 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

8 months ago
Next Post
Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

Majalisar Wakilan Jama'ar Kasar Sin, NPC Ta Amince Da Kara Shekarun Aiki Kafin Ritaya

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi GargaÉ—i Kan Cin Sabon Bashi

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi GargaÉ—i Kan Cin Sabon Bashi

May 29, 2025
ÆŠalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

ÆŠalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

May 29, 2025
Zaman lafiya

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

May 29, 2025
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

May 29, 2025
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

May 29, 2025
Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.