Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya jaddada kudirin shugaban kasa, Bola Tinubu, na tabbatar da zaman lafiya, tsaro da zaman lafiyar mashigin tekun Guinea, musamman sauye-sauyen da ake yi a hukumar da ke kula da mashigin tekun Guinea (GGC).
Ya kuma jaddada himmar Nijeriya wajen yin hadin gwiwa a yankin da kuma cika alkawuran tsarin kula da teku na shekarar 2050 da kungiyar hadin kan Afrika ta shirya.
- Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL
- Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar, mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka a ranar Talata lokacin da ya karbi bakuncin babban sakataren GGC, Mista Jose Mba Abeso, da tawagarsa a wata ziyarar ban girma da suka kai fadar shugaban kasa a Abuja.
“A madadin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ina kara tabbatar da tsayin dakar Nijeriya ga manufofin GGC. Babu wanda zai iya gurgunta rawar da hukumar ke takawa wajen samar da hadin kai, zaman lafiya, da ci gaba mai dorewa a mashigin tekun Guinea,” in ji shi.
Ya yaba wa mahukuntan GGC, yana mai ba su tabbacin cewa, “Nijeriya na nan tsayin daka kan kare manufofin hukumar.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp