ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

A yau, al’ummar kasar Sin sun gudanar da wani gagarumin gangami da faretin soji a birnin Beijing na kasar, domin tunawa da cikar shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Shugabanin wasu kasashe 26 ne suka halarci bikin tunawa da ya gudana, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin cewa, jama’ar kasar Sin za su tsaya tsayin daka wajen bin tafarki na gaskiya, wanda zai haifar da ci gaban daukacin dan Adam, da bin hanyar raya kasa cikin lumana, da yin aiki kafada da kafada da al’ummun kasashe daban daban, wajen gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya ga bil’adama.

 

Me ya sa Sinawa za su iya bin tafarki na gaskiya? Domin sun dade suna jin radadin yake-yake.

ADVERTISEMENT
  • Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti
  • Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Kasar Sin babban fagen daga ne a yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Lokacin da sojojin Japan suka fara mamaye kasar Sin a shekara ta 1931, Sinawa sun kasance na farko a duniya wajen daga tutar yaki da tafarkin murdiya. Yayin da wasu kasashen yammacin duniya ke tunanin magance yaki da ‘yan Nazi, sojoji da fararen hula na kasar Sin sun riga sun tashi haikan don yaki da maharan kasar Japan, ko da yake ba su da makamai masu inganci a lokacin.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, kasar Sin ta kasance cikin talauci da rauni, kuma sadaukarwar da Sinawa suka yi wajen kare kasarsu tana da yawa. Bisa kididdigar da aka yi, yawan sojojin kasar Sin da fararen hula na kasar da suka rasa rayuka, ko kuma suka ji rauni a yakin da suka yi da sojojin Japan ya zarce miliyan 35, inda yawan hasarar da aka samu ya haura dala biliyan 600. Al’ummar kasar Sin, bisa babbar sadaukarwar da suka yi, sun samar da damar cin nasara a yakin da jama’ar kasashe daban daban suka yi na kin tafarkin murdiya. Saboda a yayin yakin na tsawon shekaru 14 da Sinawa suka yi da maharan kasar Japan, fagen daga dake kasar Sin ya janyo hankalin kaso 60% zuwa 94% na sojojin kasa na kasar Japan. Wannan yanayi ya wargaza muradin sojojin Japan da masu bin tafarkin murdiya na kasar Jamus, na hadin gwiwa a kokarin mamaye duniya daga dukkan bangarorin gabas da yamma.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Yakin da Sinawa suka yi cikin adalci ya sa su samun karramawa, da goyon baya daga gamayyar kasa da kasa. Kana yadda al’ummun kasashe daban daban a wancan lokaci suka hada kai da juna a karkashin tutar yaki da tafarkin murdiya, ko da yake akwai bambanci a tsakaninsu ta fuskokin kasa, da kabila, da kuma akida, ya kai ga cimma nasara a yakin kin tafarkin murdiya, da tabbatar da sabon tsarin kasa da kasa bayan yakin a karshe.

Tarihin yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya ya nuna mana wasu tunani masu zurfi, wadanda jama’ar kasar Sin suka san su sosai:

Da farko dai, komai wahalhalun da aka sha, adalci zai yi galaba a kan muguntawa, haske kuma zai kori duhu. Wannan tamkar doka ce ta tarihi.

Na biyu, ‘yan Adam na da makomar bai daya. Ya kamata a samu daidaituwa, da jituwa, da cude-ni-in-cude-ka, tsakanin kasashe da kabilu daban daban, ta yadda za a samu damar tabbatar da tsaron bai daya, da kawar da yaki daga karshensa.

A zamanin da muke ciki, ana ta samun abkuwar rikice-rikice a duniya, inda dan Adam suka sake fuskantar bukatar yin zabi tsakanin cudanya da juna ko yin gaba da juna, zaman lafiya ko yaki. Sai dai kasar Sin ta riga ta samu babban ci gaba: Yanzu kasar na bikin tunawa da nasarar da ta samu ta gagarumin faretin soji. Kana a karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, jama’ar kasar na ta kokarin zamanantar da kasarsu bisa hadin kansu.

Jawabin shugaba Xi Jinping ya bayyanawa duniya cewa: Kasar Sin mai karfi za ta ci gaba da samar da gudummawa ga ci gaban al’ummar dan Adam da na tattalin arzikin duniya cikin lumana.

Bari mu yi kokarin neman samun ci gaba tare, bisa wani tafarki na gaskiya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi
  • Sulaiman
    An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

LABARAI MASU NASABA

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.