• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BVAS

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta ce, ‘yan daba sun tarwatsa aikin zabe a Jihar Delta da Katsina, inda suka yi awon gaba da na’urar tantance masu zabe BVAS har guda takwas.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai a ranar Asabar.

  • Zaben 2023: Atiku Ya Lashe Mazabar Shugaban Majalisar Dattawa A Yobe
  • Zaben 2023: Peter Obi Ya Lashe Akwatin Mazabarsa A Anambra

Ya yi bayanin cewa, a karamar hukumar Oshimili da ke jihar Delta, ‘yan daban sun kai hari rumfar zabe tare sannan suja sace na’urar BVAS guda biyu.

Kazalika, ya kara da cewa, a karamar hukumar Safana da ke Jihar Katsina, ‘yan daban sun hari kan wata cibiyar kada kuri’a tare da yin awon gaba da na’urar BVAS guda shida, amma a cewarsa jami’an tsaro sun samu nasarar kwato guda uku daga cikin shidan da aka sace.

Sannan, ya nuna takaicinsa cewa yanzu ‘yan daban siyasa sun koma harar mashin din BVAS.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Mahmood ya cigaba da cewa aikin da ke rataye a kan hukumar shi ne tabbatar an gudanar da zaben ingatacce kuma sahihi wanda zai karbu.

A cewarsa, “A karamar hukumar Oshimili da ke jihar Delta, ‘yan daba sun farmaki rumfar zabe suka sace mashinan BVAS biyu a lokacin da aikin zaben ke gudana. Amma a bisa kokarinmu, nan da nan muka samu nasarar maye gurbin na’urorin da aka sace, tare da kara jibge jami’an tsaro kuma zabe ya cigaba da gudana.

“Sannan, a karamar hukumar Safana a jihar Katsina nan ma ‘yan daba sun farmaki rumfar zabenmu tare da sace BVAS 6. Amma mun samu nasarar kwato wasu, sannan an kara zuba jami’an tsaro kuma zaben ya cigaba da gudana kamar yadda aka tsara a wannan wurin.”

Ya ce, wannan shine karo na farko tun babban zaben 2011 da aka sanya zabe aka gudanar ba tare da dagewa ba.

“Mun tabbatar mun dage wajen cigaba da gudanar da abubuwan da suka dace. Zuwa yanzu mun samu nasarori sosai a yayin zaben nan kuma hanyar amfani da na’urar BVAS an samu aiki mai inganci.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Next Post
Firaministan Sin Ya Bukaci A Karfafa Ci Gaba Da Kuma Daidaita Farashin Kayayyaki

Firaministan Sin Ya Bukaci A Karfafa Ci Gaba Da Kuma Daidaita Farashin Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
BVAS

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.