• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnoni: Za Mu Gyara Duk Matsalolin Da Aka Samu A Zaben Shugaban Kasa – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Zaben Mazabar Dan Majalisar Tarayya Na Kabba/Bunu/Ijumu Ta Kogi Bai Kammalu Ba —INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa INEC za ta yi dukkan abin da za ta iya domin tabbatar da a lokacin zaɓen gwamnoni an kauce wa maimaita duk wasu cikas ɗin da aka fuskata lokacin zaɓen shugaban shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

 

Yakubu ya yi wannan jaddadawa ce a lokacin da ya ke taro da Kwamishinonin Zaɓe na Ƙasa, domin bibiya da nazarin yadda hukumar ta gudanar da zaɓen 25 ga Fabrairu, 2023.

  • INEC Za Ta Bai Wa Tinubu Takardar Shaidar Lashe Zabe Da Yamma

Ya ce maƙasudin taron na su shi ne a tattauna cikas ɗin da aka samu da kuma tabbatar da cewa ba a sake maimaita faruwar haka a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi ba, wanda za a gudanar a ranar 11 ga Maris, 2023.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Babu shakka zaɓen da aka gudanar a satin da ya gabata ya samu cikas da ƙalubalen da ke buƙatar magancewa da kuma hana sake afkuwar su da gaggawa. An ɗauki lokaci tare da shan matuƙar walaha wajen tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓe. Amma dai an fuskanci cikas wajen aiwatarwa.

 

“Waɗansu ƙalubalen da aka ci karo da su, bagatatan su ka faru, ba a yi zato ko tunanin hakan zai iya faruwa ba. Musamman matsalolin aikawa da kayan zaɓe, na’urorin sadarwa da tsarin fasahar zamani, halayyar wasu jami’an zaɓe, ɗabi’un wasu ejan-ejan na jam’iyyu da masu goyon bayan jam’iyyun sun ƙara kawo wa tsarin tafiyar da shirin naƙasu ko cikas.”

 

Yayin da ya ke yaba wa irin jajircewar da ‘yan Nijeriya su ka yi da halin dattakon da wasu shugabannin siyasa su ka nuna, Yakubu ya ce abin da ya faru a lokacin zaɓe ya zama wani babban darasi ga INEC, ta yadda ta gaggauta gano matsalolin da su ka faru, domin kauce wa sake faruwar irin haka a zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki ta jihohi, wanda za a yi zaɓen gwamnoni a jihohi 28, kuma za a zaɓi ‘yan majalisar dokoki har 996.

 

Yakubu ya ce a zaɓen ranar tilas ma’aikatan INEC su zage damtse sosai a lokacin zaɓen ranar 11 ga Maris.

 

“Duk ma’aikacin da aka kama ya na wasa ko rashin ɗaukar aikin sa da muhimmanci, ko na dindindin ne ko na wucin-gadi a lokacin zaɓen shugaban ƙasa, to kada a kuskura a bar shi ya yi aikin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokoki.

 

“Tilas kuma ya kasance an kai kayan zaɓe kwanaki kafin ranar zaɓe a dukkan ƙananan hukumomi.

 

“Kwamishinonin Zaɓe da aka tura jihohi za a ɗora wa laifin rashin kai kayan zaɓe zuwa ƙananan hukimomi da wuri. Haka babu wani dalilin da za a ƙi kai janareto a cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.”

 

Yakubu ya ce za a tabbatar an yi amfani da na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS a ranar zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihohi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

Next Post

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

1 hour ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.