• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnoni: Za Mu Gyara Duk Matsalolin Da Aka Samu A Zaben Shugaban Kasa – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Zaben Mazabar Dan Majalisar Tarayya Na Kabba/Bunu/Ijumu Ta Kogi Bai Kammalu Ba —INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa INEC za ta yi dukkan abin da za ta iya domin tabbatar da a lokacin zaɓen gwamnoni an kauce wa maimaita duk wasu cikas ɗin da aka fuskata lokacin zaɓen shugaban shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

 

Yakubu ya yi wannan jaddadawa ce a lokacin da ya ke taro da Kwamishinonin Zaɓe na Ƙasa, domin bibiya da nazarin yadda hukumar ta gudanar da zaɓen 25 ga Fabrairu, 2023.

  • INEC Za Ta Bai Wa Tinubu Takardar Shaidar Lashe Zabe Da Yamma

Ya ce maƙasudin taron na su shi ne a tattauna cikas ɗin da aka samu da kuma tabbatar da cewa ba a sake maimaita faruwar haka a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi ba, wanda za a gudanar a ranar 11 ga Maris, 2023.

 

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

“Babu shakka zaɓen da aka gudanar a satin da ya gabata ya samu cikas da ƙalubalen da ke buƙatar magancewa da kuma hana sake afkuwar su da gaggawa. An ɗauki lokaci tare da shan matuƙar walaha wajen tsare-tsaren yadda za a gudanar da zaɓe. Amma dai an fuskanci cikas wajen aiwatarwa.

 

“Waɗansu ƙalubalen da aka ci karo da su, bagatatan su ka faru, ba a yi zato ko tunanin hakan zai iya faruwa ba. Musamman matsalolin aikawa da kayan zaɓe, na’urorin sadarwa da tsarin fasahar zamani, halayyar wasu jami’an zaɓe, ɗabi’un wasu ejan-ejan na jam’iyyu da masu goyon bayan jam’iyyun sun ƙara kawo wa tsarin tafiyar da shirin naƙasu ko cikas.”

 

Yayin da ya ke yaba wa irin jajircewar da ‘yan Nijeriya su ka yi da halin dattakon da wasu shugabannin siyasa su ka nuna, Yakubu ya ce abin da ya faru a lokacin zaɓe ya zama wani babban darasi ga INEC, ta yadda ta gaggauta gano matsalolin da su ka faru, domin kauce wa sake faruwar irin haka a zaɓen gwamnoni da na majalisar dokoki ta jihohi, wanda za a yi zaɓen gwamnoni a jihohi 28, kuma za a zaɓi ‘yan majalisar dokoki har 996.

 

Yakubu ya ce a zaɓen ranar tilas ma’aikatan INEC su zage damtse sosai a lokacin zaɓen ranar 11 ga Maris.

 

“Duk ma’aikacin da aka kama ya na wasa ko rashin ɗaukar aikin sa da muhimmanci, ko na dindindin ne ko na wucin-gadi a lokacin zaɓen shugaban ƙasa, to kada a kuskura a bar shi ya yi aikin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokoki.

 

“Tilas kuma ya kasance an kai kayan zaɓe kwanaki kafin ranar zaɓe a dukkan ƙananan hukumomi.

 

“Kwamishinonin Zaɓe da aka tura jihohi za a ɗora wa laifin rashin kai kayan zaɓe zuwa ƙananan hukimomi da wuri. Haka babu wani dalilin da za a ƙi kai janareto a cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.”

 

Yakubu ya ce za a tabbatar an yi amfani da na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS a ranar zaɓen gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihohi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

Next Post

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Related

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

1 hour ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

2 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

3 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

5 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.