• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

byAbdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Kano

A yayin da zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a Jihar Kano ke kara karatowa, ‘yan takara sai karuwa suke yi, musamman ma a jam’iyya mai mulki ta NNPP, wanda yanzu haka akwai masu shawa’ar shugabancin kananan hukumomin 44 da suka haura mutum 400, inda kusan kowacce karamar hukuma ke da akallah masu zawarcin kujerar sama da mutum 20.

Wannan ambaliyar ‘yan takara a karkashin tutar jam’iyya mai mulki baya rasa nasa ba da irin salon jagoran darikar Kwankwasiyya, Rabiu Masu Kwankwaso wanda a baya a lokacin mulkinsa ya bayyana cewa, ‘kazarsa ta yi kwai 44 kuma ba za ta yi baragurbi ba’, hakan ta sa wasu ke ganin irin wannan za a maimaita a kakar zaben mai zuwa.

  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Wata Mata Da ‘Ya’yanta Biyu Bayan Ruftawar Gini A Kano

Sai dai kuma a wannan karo ana ganin kila a fuskanci turjiya, domin tun yanzu an fara jin bullar wasu ‘yan takara da ake kira da ‘yan takarar Miller da kuma wasu da ake wa lakabi da Abba tsaya da kafarka.

Wannan kuma baya rasa nasaba da irin dabaibayin da jagoran Kwankwasiyyar ya yi wa Gwamnatin Abba Kabir Yusuf. Wadda wasu ke ganin gwamnan ba shi da wani katabus kan abin da ya shafi tsayar da ‘yan takara, domin hakan ta faru a baya a lokacin nada kantomin riko, wanda Gwamna Abba na kasar Saudiyya aka yi kuma aka gama.

Wata majiya ta tsegunta wa Jaridar LEADERSHIP HAUSA cewa, ana zargin ware wasu mutane uku da ake ganin su ne za su yi uwa kuma su yi makarbiya wajen tsayar da dukkanin ‘yan takara, musamman a wuraren da aka kasa samun maslaha.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Haka kuma batun maslahar ma ana ginin maslaha ce ko a sa a baka. Domin an fara jin wasu na fara tanadar kudin na gani ina so domin mika wa masu ido da kwalli.

Amma kuma dole sai jam’iyyar NNPP ta yi karatun ta nutsu, domin jam’iyyun adawa, musamman jam’iyyar APC da takwararta ta PDP na ganin sahun gwamanti mai mulki a Kano ya shiga rafkanuwa, musamman idan aka yi la’akari da badakalar kudade da ke kara bayyana wadda ake zargin wasu na kusa da gwamnati da hannu a ciki dumu-dumu.

Wadannan matsaloli da su ne jam’iyyun adawa za su matsa a lokacin yakin neman zabe, sai kuma batun masarautu da aka mayar da sarakuna masu daraja ta biyu a birnin na Kano, ita ma wannan matsala za ta yi tasiri, musamman a yankunan da suka fara amfanar sabbin masarautun wadanda bayan shigowar gwamnati NNPP ta rushe su tare da mayar da su masu daraja ta biyu, wanda hakan ya yi matukar fusata mazauna wadannan yankuna.

Haka ma batun kudaden tsayawa takara da hukumar zabe mai zaman kanta a Kano ta ayyana, na nuni da wani shiri na hana duk wani mai karamin karfi ko wadanda ba su da gwamnati samun damar shiga takarar a dama da su sakamakon tsawwala kudaden takarar, inda aka a je naira miliyon 10 a matsayin kudin na gani ina so ga duk mai bukatar tsayawa takarar kujerar shugabancin karamar hukuma zai biya, yayin da kansila kuma zai biya naira miliyon 5 lakadan.

Wasu na ganin jam’iyyar NNPP za ta yi amfani da karfin ikon da ke hannunta wajen saya wa duk wadanda suka tsayar takara fom, yayin da sauran jam’yyun da ba su da mulki ana ganin an takura musu.

Wannan ta sa yanzu haka wasu gamayyar kungiyoyi ke shirin gurfanar da hukumar zaben mai zaman kanta ta Jihar Kano a gaban kotu domin bin ba’asin tsawwala kudazen takarar.

Koma dai me ake ciki ‘yan makonni kadan suka rage domin gudanar da zaben fid da gwani, wanda sakamakonsa ne zai nuna wa saura jam’iyyun makomarsu da kuma ‘yan takara da ba su da uwa a gindin murhun jam’iyya mai mulki, wanda ake kyautata zaton za a yi bari wanda jam’iyyun adawa za su daka wasoson su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version