• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP

by Abdullahi Muh'd Sheka
10 months ago
in Siyasa
0
Zaben Kananan Hukumomin Kano: ‘Yan Takara 400 Na Tururuwar Kamun Kafa A NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a Jihar Kano ke kara karatowa, ‘yan takara sai karuwa suke yi, musamman ma a jam’iyya mai mulki ta NNPP, wanda yanzu haka akwai masu shawa’ar shugabancin kananan hukumomin 44 da suka haura mutum 400, inda kusan kowacce karamar hukuma ke da akallah masu zawarcin kujerar sama da mutum 20.

Wannan ambaliyar ‘yan takara a karkashin tutar jam’iyya mai mulki baya rasa nasa ba da irin salon jagoran darikar Kwankwasiyya, Rabiu Masu Kwankwaso wanda a baya a lokacin mulkinsa ya bayyana cewa, ‘kazarsa ta yi kwai 44 kuma ba za ta yi baragurbi ba’, hakan ta sa wasu ke ganin irin wannan za a maimaita a kakar zaben mai zuwa.

  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Wata Mata Da ‘Ya’yanta Biyu Bayan Ruftawar Gini A Kano

Sai dai kuma a wannan karo ana ganin kila a fuskanci turjiya, domin tun yanzu an fara jin bullar wasu ‘yan takara da ake kira da ‘yan takarar Miller da kuma wasu da ake wa lakabi da Abba tsaya da kafarka.

Wannan kuma baya rasa nasaba da irin dabaibayin da jagoran Kwankwasiyyar ya yi wa Gwamnatin Abba Kabir Yusuf. Wadda wasu ke ganin gwamnan ba shi da wani katabus kan abin da ya shafi tsayar da ‘yan takara, domin hakan ta faru a baya a lokacin nada kantomin riko, wanda Gwamna Abba na kasar Saudiyya aka yi kuma aka gama.

Wata majiya ta tsegunta wa Jaridar LEADERSHIP HAUSA cewa, ana zargin ware wasu mutane uku da ake ganin su ne za su yi uwa kuma su yi makarbiya wajen tsayar da dukkanin ‘yan takara, musamman a wuraren da aka kasa samun maslaha.

Labarai Masu Nasaba

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Haka kuma batun maslahar ma ana ginin maslaha ce ko a sa a baka. Domin an fara jin wasu na fara tanadar kudin na gani ina so domin mika wa masu ido da kwalli.

Amma kuma dole sai jam’iyyar NNPP ta yi karatun ta nutsu, domin jam’iyyun adawa, musamman jam’iyyar APC da takwararta ta PDP na ganin sahun gwamanti mai mulki a Kano ya shiga rafkanuwa, musamman idan aka yi la’akari da badakalar kudade da ke kara bayyana wadda ake zargin wasu na kusa da gwamnati da hannu a ciki dumu-dumu.

Wadannan matsaloli da su ne jam’iyyun adawa za su matsa a lokacin yakin neman zabe, sai kuma batun masarautu da aka mayar da sarakuna masu daraja ta biyu a birnin na Kano, ita ma wannan matsala za ta yi tasiri, musamman a yankunan da suka fara amfanar sabbin masarautun wadanda bayan shigowar gwamnati NNPP ta rushe su tare da mayar da su masu daraja ta biyu, wanda hakan ya yi matukar fusata mazauna wadannan yankuna.

Haka ma batun kudaden tsayawa takara da hukumar zabe mai zaman kanta a Kano ta ayyana, na nuni da wani shiri na hana duk wani mai karamin karfi ko wadanda ba su da gwamnati samun damar shiga takarar a dama da su sakamakon tsawwala kudaden takarar, inda aka a je naira miliyon 10 a matsayin kudin na gani ina so ga duk mai bukatar tsayawa takarar kujerar shugabancin karamar hukuma zai biya, yayin da kansila kuma zai biya naira miliyon 5 lakadan.

Wasu na ganin jam’iyyar NNPP za ta yi amfani da karfin ikon da ke hannunta wajen saya wa duk wadanda suka tsayar takara fom, yayin da sauran jam’yyun da ba su da mulki ana ganin an takura musu.

Wannan ta sa yanzu haka wasu gamayyar kungiyoyi ke shirin gurfanar da hukumar zaben mai zaman kanta ta Jihar Kano a gaban kotu domin bin ba’asin tsawwala kudazen takarar.

Koma dai me ake ciki ‘yan makonni kadan suka rage domin gudanar da zaben fid da gwani, wanda sakamakonsa ne zai nuna wa saura jam’iyyun makomarsu da kuma ‘yan takara da ba su da uwa a gindin murhun jam’iyya mai mulki, wanda ake kyautata zaton za a yi bari wanda jam’iyyun adawa za su daka wasoson su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoNNPPZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsin Rayuwa: Duk Da Ƙaruwar KuÉ—in Shigar Nijeriya, Akwai Sauran Jan Aiki – Masana

Next Post

Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

Related

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

1 day ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

1 day ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

1 day ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

3 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

3 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

3 days ago
Next Post
Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

Wainar Da Aka Toya A Taron ‘Yan Jarida Na Hausa A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.