• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zainab Youssef: Mace Ta Farko Da Ta Samu Lasisin Injiniyar Jiragen Sama A Sudan

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Zainab Youssef

Zainab A – Obaid Youssef ta kasance mace Injiniyar Jiragen Sama a kasar Sudan daga (1952 zuwa 19 ga Maris, 2016), kuma ita ce mace ta farko da ta samu lasisin haka daga hukumar kula da sufurin jiragen sama ta kasar Birtaniya.

Ta yi aiki a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan daga Yulin 1973 zuwa Mayun 1992 wanda bayan nan ta koma Birtaniya da zama. A shekarun 1960, matan Sudan da ke kokarin karatu da aiki a wasu bangarori ciki har da sashen injiniya sun gamu da tasku saboda yanayin al’adun mutanen kasar. Sai dai duk da haka, Zainab ta jajirce har ta yi karatu da kuma aiki a bangaren da ya shafi lantarki da aikin injiniyar jiragen sama. Daga nau’o’in jiragen da Zainab ta yi aiki a kansu akwai samfurin Boeing 707, Boeing 737/347/Boker 50 da Boker F27 duk a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan, sai kuma samfurin Cessna 402/404/208 da kuma Bitchcraft 1900 na Kamfanin Kudancin Landan.

  • Kungiya Ta Shirya Taro Kan Na Bunkasa Kimiyyar Karatu Daga Nesa
  • Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

An haifi Zainab a Birnin Khartoum a ranar 23 ga watan Yuni a shekara ta 1952. Ita ce ‘ya ta farko ga mahaifinta Al-Abeed Yaussef Ahmed Shadewan, sanannen dan kasuwa da ake matukar girmamawa a Birnin, iyayenta, uwa da uba duk sun kasance masu riko da addini.

Ta taso ce a kauyen Um Dawa Ban da ya yi fice da Makarantar Al Masid, katafariyar makarantar koyar da Alkur’ani mai girma ga yara maza inda mutane a daukacin Sudan da yankin sahara na kudancin Afirka ke tururuwar kai ‘ya`yansu domin koyon karatun Alkur’ani. Zainab ta kammala karatunta na matakin Sakandare bisa kwarin gwiwar da ta samu daga mahaifinta, saboda a wancan lokacin bisa al’adar Sudan, yarinya mai irin shekarunta kan dakatar da karatun da take yi ta yi aure.

Zainab dai ba ta tsaya ba har sai da ta cimma burinta na karanta fannin aikin Injiniyan lantarki a Jami’ar Khartoum daga shekarar 1970 zuwa 1973.

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ta yi aiki a matsayin Injiniyar Jiragen Sama a sashen gyara na’urori. Daga 1983 zuwa 1986 kuma, ta koma karatu domin nazarin aikin babbar injiniyar jiragen sama da lantarki a Kwalejin Kere-kere ta Brunel da ke Bristol a Birtaniya, inda ta samu lasisin aiki daga Hukumar Jiragen Sama ta Birtaniya. A shekara ta 1990 ta samu digiri na biyu a fannin nazarin sarrafa kayayyaki mai zurfi daga Jami’ar Kingston.

Wannan kadan kenan daga Tarihin Injiniya Zainab kamar yadda muka nakalto daga kafar nazarin al’amuran mata na Sudan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
NAHCON

Kungiya Ta Bukaci NAHCON Ta Sanar Da Ranar Da Za A Fara Jigilar Alhazai Na 2024

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.