• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zainab Youssef: Mace Ta Farko Da Ta Samu Lasisin Injiniyar Jiragen Sama A Sudan

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Zainab Youssef: Mace Ta Farko Da Ta Samu Lasisin Injiniyar Jiragen Sama A Sudan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zainab A – Obaid Youssef ta kasance mace Injiniyar Jiragen Sama a kasar Sudan daga (1952 zuwa 19 ga Maris, 2016), kuma ita ce mace ta farko da ta samu lasisin haka daga hukumar kula da sufurin jiragen sama ta kasar Birtaniya.

Ta yi aiki a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan daga Yulin 1973 zuwa Mayun 1992 wanda bayan nan ta koma Birtaniya da zama. A shekarun 1960, matan Sudan da ke kokarin karatu da aiki a wasu bangarori ciki har da sashen injiniya sun gamu da tasku saboda yanayin al’adun mutanen kasar. Sai dai duk da haka, Zainab ta jajirce har ta yi karatu da kuma aiki a bangaren da ya shafi lantarki da aikin injiniyar jiragen sama. Daga nau’o’in jiragen da Zainab ta yi aiki a kansu akwai samfurin Boeing 707, Boeing 737/347/Boker 50 da Boker F27 duk a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan, sai kuma samfurin Cessna 402/404/208 da kuma Bitchcraft 1900 na Kamfanin Kudancin Landan.

  • Kungiya Ta Shirya Taro Kan Na Bunkasa Kimiyyar Karatu Daga Nesa
  • Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

An haifi Zainab a Birnin Khartoum a ranar 23 ga watan Yuni a shekara ta 1952. Ita ce ‘ya ta farko ga mahaifinta Al-Abeed Yaussef Ahmed Shadewan, sanannen dan kasuwa da ake matukar girmamawa a Birnin, iyayenta, uwa da uba duk sun kasance masu riko da addini.

Ta taso ce a kauyen Um Dawa Ban da ya yi fice da Makarantar Al Masid, katafariyar makarantar koyar da Alkur’ani mai girma ga yara maza inda mutane a daukacin Sudan da yankin sahara na kudancin Afirka ke tururuwar kai ‘ya`yansu domin koyon karatun Alkur’ani. Zainab ta kammala karatunta na matakin Sakandare bisa kwarin gwiwar da ta samu daga mahaifinta, saboda a wancan lokacin bisa al’adar Sudan, yarinya mai irin shekarunta kan dakatar da karatun da take yi ta yi aure.

Zainab dai ba ta tsaya ba har sai da ta cimma burinta na karanta fannin aikin Injiniyan lantarki a Jami’ar Khartoum daga shekarar 1970 zuwa 1973.

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Ta yi aiki a matsayin Injiniyar Jiragen Sama a sashen gyara na’urori. Daga 1983 zuwa 1986 kuma, ta koma karatu domin nazarin aikin babbar injiniyar jiragen sama da lantarki a Kwalejin Kere-kere ta Brunel da ke Bristol a Birtaniya, inda ta samu lasisin aiki daga Hukumar Jiragen Sama ta Birtaniya. A shekara ta 1990 ta samu digiri na biyu a fannin nazarin sarrafa kayayyaki mai zurfi daga Jami’ar Kingston.

Wannan kadan kenan daga Tarihin Injiniya Zainab kamar yadda muka nakalto daga kafar nazarin al’amuran mata na Sudan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Wallafa Littafi Game Da Bayanan Xi Game Da Shawarar BRI Na Harshen Turanci

Next Post

Kungiya Ta Bukaci NAHCON Ta Sanar Da Ranar Da Za A Fara Jigilar Alhazai Na 2024

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 weeks ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

1 month ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

4 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

6 months ago
Next Post
NAHCON

Kungiya Ta Bukaci NAHCON Ta Sanar Da Ranar Da Za A Fara Jigilar Alhazai Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Zainab Youssef

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.