• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zainab Youssef: Mace Ta Farko Da Ta Samu Lasisin Injiniyar Jiragen Sama A Sudan

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Zainab Youssef: Mace Ta Farko Da Ta Samu Lasisin Injiniyar Jiragen Sama A Sudan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zainab A – Obaid Youssef ta kasance mace Injiniyar Jiragen Sama a kasar Sudan daga (1952 zuwa 19 ga Maris, 2016), kuma ita ce mace ta farko da ta samu lasisin haka daga hukumar kula da sufurin jiragen sama ta kasar Birtaniya.

Ta yi aiki a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan daga Yulin 1973 zuwa Mayun 1992 wanda bayan nan ta koma Birtaniya da zama. A shekarun 1960, matan Sudan da ke kokarin karatu da aiki a wasu bangarori ciki har da sashen injiniya sun gamu da tasku saboda yanayin al’adun mutanen kasar. Sai dai duk da haka, Zainab ta jajirce har ta yi karatu da kuma aiki a bangaren da ya shafi lantarki da aikin injiniyar jiragen sama. Daga nau’o’in jiragen da Zainab ta yi aiki a kansu akwai samfurin Boeing 707, Boeing 737/347/Boker 50 da Boker F27 duk a Kamfanin Jiragen Sama na Sudan, sai kuma samfurin Cessna 402/404/208 da kuma Bitchcraft 1900 na Kamfanin Kudancin Landan.

  • Kungiya Ta Shirya Taro Kan Na Bunkasa Kimiyyar Karatu Daga Nesa
  • Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

An haifi Zainab a Birnin Khartoum a ranar 23 ga watan Yuni a shekara ta 1952. Ita ce ‘ya ta farko ga mahaifinta Al-Abeed Yaussef Ahmed Shadewan, sanannen dan kasuwa da ake matukar girmamawa a Birnin, iyayenta, uwa da uba duk sun kasance masu riko da addini.

Ta taso ce a kauyen Um Dawa Ban da ya yi fice da Makarantar Al Masid, katafariyar makarantar koyar da Alkur’ani mai girma ga yara maza inda mutane a daukacin Sudan da yankin sahara na kudancin Afirka ke tururuwar kai ‘ya`yansu domin koyon karatun Alkur’ani. Zainab ta kammala karatunta na matakin Sakandare bisa kwarin gwiwar da ta samu daga mahaifinta, saboda a wancan lokacin bisa al’adar Sudan, yarinya mai irin shekarunta kan dakatar da karatun da take yi ta yi aure.

Zainab dai ba ta tsaya ba har sai da ta cimma burinta na karanta fannin aikin Injiniyan lantarki a Jami’ar Khartoum daga shekarar 1970 zuwa 1973.

Labarai Masu Nasaba

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Ta yi aiki a matsayin Injiniyar Jiragen Sama a sashen gyara na’urori. Daga 1983 zuwa 1986 kuma, ta koma karatu domin nazarin aikin babbar injiniyar jiragen sama da lantarki a Kwalejin Kere-kere ta Brunel da ke Bristol a Birtaniya, inda ta samu lasisin aiki daga Hukumar Jiragen Sama ta Birtaniya. A shekara ta 1990 ta samu digiri na biyu a fannin nazarin sarrafa kayayyaki mai zurfi daga Jami’ar Kingston.

Wannan kadan kenan daga Tarihin Injiniya Zainab kamar yadda muka nakalto daga kafar nazarin al’amuran mata na Sudan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Wallafa Littafi Game Da Bayanan Xi Game Da Shawarar BRI Na Harshen Turanci

Next Post

Kungiya Ta Bukaci NAHCON Ta Sanar Da Ranar Da Za A Fara Jigilar Alhazai Na 2024

Related

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

3 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

4 weeks ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

7 months ago
Next Post
NAHCON

Kungiya Ta Bukaci NAHCON Ta Sanar Da Ranar Da Za A Fara Jigilar Alhazai Na 2024

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.