ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sa hannu a kan wani shirin dokar samar da gudummawa ga kasashen ketare da ya kunshi dala biliyan 95, bayan da majalisun dokokin kasar suka zartas da shi. An ce, daga cikinsa, za a ware gudummawar da ta kai biliyan 60.8 ga Ukraine da ma biliyan 26 ga Isra’ila, baya ga dala biliyan 8 da za a samar ga yankin Asiya da tekun Pasifik da sunan wai tabbatar da“tsaron yankin Indo-Pasifik”. Daga nan kuma, shirin dokar ya fara aiki a hukumance. Bayan da ya sa hannu a dokar, shugaba Biden ya bayyana cewa, za a fara jigilar makamai da kudinsu ya kai dala biliyan daya zuwa Ukraine cikin wasu sa’o’i kadan. 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai game da zartas da shirin dokar da aka yi, shugaban majalisar wakilai ta kasar Amurka, Mike Johnson ya bayyana cewa, “Babu kwanciyar hankali a duniyarmu, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce, don haka muka yi kokari, kuma ina ganin tarihi zai ba da amsa.” To, amma ko da gaske ne abin haka yake kamar yadda ‘yan siyasar Amurka irinsu Mr. Mike Johnson suka fada?

  • Kasar Sin Ta Shirya Harba Na’urar Binciken Wata Ta Chang’e-6 
  • Shugabannin Sin Da Tanzaniya Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Huldar Diplomasiyyar Kasashen Su

Babu shakka, duniyarmu na fama da tashe-tashen hankali. Rikici na ci gaba a tsakanin Rasha da Ukraine sama da shekaru biyu bayan barkewarsa, ga kuma tabarbarewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda har ya haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen shiyyar. Yake-yake sun haifar da munanan hasarorin rayuka da kuma matsalolin jin kai. A kan ce, babu wanda ya ci nasara a fagen yaki. Amma bayan fagen yaki, akwai kasar da ke cin kazamar riba. Bisa kididdigar da aka samar, an ce, gudummawar da Amurka ta samar wa Ukraine ta kai dala biliyan 43.7 tun bayan barkewar rikicin a shekarar 2022, sai kuma a watan Nuwamban bara, majalisun dokokin Amurka sun amince da samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 14.3 ga Isra’ila. Amma a hakika, duk da cewa gudummawa ce ga kasashen ketare, amma akasarin kudaden sun shiga aljihun masu sayar da makamai na kasar ta Amurka ne. A wannan karo ma, daga cikin dala biliyan 60.8 da ta samar wa Ukraine, akwai dala biliyan 27.6 da aka ware musamman domin sayen makamai da tsarin kandagarkin makamai daga Amurka, kwatankwacin dala biliyan 9 ne kawai da aka ware wajen samar da gudummawar jin kai da farfado da tattalin arziki a kasar Ukraine.

ADVERTISEMENT

Abin lura kuma shi ne, shirin dokar ta kuma tsara samar da dala biliyan 8.12 don “tinkarar matakan da babban yankin kasar Sin za ta dauka a yankin Indo-Pasifik”. Daga cikinsu kuwa, an ware dala biliyan 1.9 don samar da kayayyakin tsaro da ma hidimomi ga yankin Taiwan da ma sauran kawayen kasar Amurka da ke yankin. Babu shakka, hakan ya saba wa sanarwoyi guda uku da kasashen Sin da Amurka suka bayar cikin hadin gwiwa, kuma katsalanda ce a cikin harkokin gidan kasar Sin, wanda kuma ya isar da sakon da bai dace ba ga mahukuntan yankin Taiwan tare da tona mana asirin Amurka game da mugun burin da take son cimmawa a yankin Asiya da tekun Pasifik. Lallai Amurka ta yi ta kalubalantar kasar Sin a kan batun Taiwan da tekun kudancin kasar Sin, don tsananta sabani a yankin, ta yadda mahukuntan yankin Taiwan da ma sauran “kawayenta” na yankin za su ba ta hadin kai wajen cimma burinta.

Amurka na daukar kanta a matsayin kasar da ta fi samar da gudummawa ga kasashen ketare. Amma a hakika, kullum tana samar da gudummawa ce don habaka cimma moriyarta da kiyaye babakeren da ta kafa a duniya, wadda ta haifar da mummunan tasiri ga zaman lafiya da ci gaba a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Kamar yadda Mr.Mike Johnson ya fada, “Babu kwanciyar hankali a duniya, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce.” Sai dai abin da Amurka ke yi na cinna wuta ga albarusan. Gudummawar nan ta dala biliyan 95, ta sake shaida wa duniya ainihin abin da ke kunshe a cikin gudummawar da Amurka ke samarwa duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.