ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sa hannu a kan wani shirin dokar samar da gudummawa ga kasashen ketare da ya kunshi dala biliyan 95, bayan da majalisun dokokin kasar suka zartas da shi. An ce, daga cikinsa, za a ware gudummawar da ta kai biliyan 60.8 ga Ukraine da ma biliyan 26 ga Isra’ila, baya ga dala biliyan 8 da za a samar ga yankin Asiya da tekun Pasifik da sunan wai tabbatar da“tsaron yankin Indo-Pasifik”. Daga nan kuma, shirin dokar ya fara aiki a hukumance. Bayan da ya sa hannu a dokar, shugaba Biden ya bayyana cewa, za a fara jigilar makamai da kudinsu ya kai dala biliyan daya zuwa Ukraine cikin wasu sa’o’i kadan. 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai game da zartas da shirin dokar da aka yi, shugaban majalisar wakilai ta kasar Amurka, Mike Johnson ya bayyana cewa, “Babu kwanciyar hankali a duniyarmu, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce, don haka muka yi kokari, kuma ina ganin tarihi zai ba da amsa.” To, amma ko da gaske ne abin haka yake kamar yadda ‘yan siyasar Amurka irinsu Mr. Mike Johnson suka fada?

  • Kasar Sin Ta Shirya Harba Na’urar Binciken Wata Ta Chang’e-6 
  • Shugabannin Sin Da Tanzaniya Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Huldar Diplomasiyyar Kasashen Su

Babu shakka, duniyarmu na fama da tashe-tashen hankali. Rikici na ci gaba a tsakanin Rasha da Ukraine sama da shekaru biyu bayan barkewarsa, ga kuma tabarbarewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda har ya haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen shiyyar. Yake-yake sun haifar da munanan hasarorin rayuka da kuma matsalolin jin kai. A kan ce, babu wanda ya ci nasara a fagen yaki. Amma bayan fagen yaki, akwai kasar da ke cin kazamar riba. Bisa kididdigar da aka samar, an ce, gudummawar da Amurka ta samar wa Ukraine ta kai dala biliyan 43.7 tun bayan barkewar rikicin a shekarar 2022, sai kuma a watan Nuwamban bara, majalisun dokokin Amurka sun amince da samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 14.3 ga Isra’ila. Amma a hakika, duk da cewa gudummawa ce ga kasashen ketare, amma akasarin kudaden sun shiga aljihun masu sayar da makamai na kasar ta Amurka ne. A wannan karo ma, daga cikin dala biliyan 60.8 da ta samar wa Ukraine, akwai dala biliyan 27.6 da aka ware musamman domin sayen makamai da tsarin kandagarkin makamai daga Amurka, kwatankwacin dala biliyan 9 ne kawai da aka ware wajen samar da gudummawar jin kai da farfado da tattalin arziki a kasar Ukraine.

ADVERTISEMENT

Abin lura kuma shi ne, shirin dokar ta kuma tsara samar da dala biliyan 8.12 don “tinkarar matakan da babban yankin kasar Sin za ta dauka a yankin Indo-Pasifik”. Daga cikinsu kuwa, an ware dala biliyan 1.9 don samar da kayayyakin tsaro da ma hidimomi ga yankin Taiwan da ma sauran kawayen kasar Amurka da ke yankin. Babu shakka, hakan ya saba wa sanarwoyi guda uku da kasashen Sin da Amurka suka bayar cikin hadin gwiwa, kuma katsalanda ce a cikin harkokin gidan kasar Sin, wanda kuma ya isar da sakon da bai dace ba ga mahukuntan yankin Taiwan tare da tona mana asirin Amurka game da mugun burin da take son cimmawa a yankin Asiya da tekun Pasifik. Lallai Amurka ta yi ta kalubalantar kasar Sin a kan batun Taiwan da tekun kudancin kasar Sin, don tsananta sabani a yankin, ta yadda mahukuntan yankin Taiwan da ma sauran “kawayenta” na yankin za su ba ta hadin kai wajen cimma burinta.

Amurka na daukar kanta a matsayin kasar da ta fi samar da gudummawa ga kasashen ketare. Amma a hakika, kullum tana samar da gudummawa ce don habaka cimma moriyarta da kiyaye babakeren da ta kafa a duniya, wadda ta haifar da mummunan tasiri ga zaman lafiya da ci gaba a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Kamar yadda Mr.Mike Johnson ya fada, “Babu kwanciyar hankali a duniya, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce.” Sai dai abin da Amurka ke yi na cinna wuta ga albarusan. Gudummawar nan ta dala biliyan 95, ta sake shaida wa duniya ainihin abin da ke kunshe a cikin gudummawar da Amurka ke samarwa duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

 

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.