• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

by Abubakar Abba
1 year ago
Sanusi

Wasu Malaman addinin Kirista da suka fito daga Arewacin Nijeriya sun kai wa Sarkin Kano na 14 kuma Khalifan Tijjaniyya a Nijeriya, Sanusi Lamido Sanusi ziyarar ban girma a gidansa da ke jihar Kaduna.

Malaman sun kai ziyarar ce da nufin kara karfafa wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiya addinin Musulunci da na Kirista.

  • Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
  • Yadda CBN Ya Karya Darajar Naira – Sanusi

Babban Limanin Cocin Christ Ebangelical and Life Interbention Ministry da ke a Jihar Kaduna, Dakta Yohanna Buru ne ya jagoranci tawagar. Haka zalika, sun kai ziyarar ce domin jaddada muhimmancin martaba addinan juna da kara hadin kai a tsakanin mabiya addinai.

A jawabinsa, Buru ya jinjina wa Khalifa musamman a kan irin gudunmawar da yake ci gaba da bayarwa na wanzar da zaman lafiya don ci gaban kasar nan.

A cewar sa, Khalifa ya jima yana dabbaka wanzar da zaman lafiya da yada girmama addinan biyu da shigewa kan gaba wajen tattanawa ko yin muhara a kan zaman lafiya ba a Nijeriya kawai ba, har ma a daukacin fadin Nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Tawagar ta kuma yaba masa a kan namijin kokarin da yake ci gaba da yi, na yada zaman lafiya, mussamman kan gudunmawar da ya bayar na lalubo da mafita kan takaddamar kungiyar ECOWAS biyo bayan kifar da gwamnatin farar hula da sojin jamhuriyar Nijar suka yi a watannin baya, wanda suka yi nuni da cewa, wannan kokarin nasa ya cancanci a karrama shi da babbar lambar yabo ta duniya ta wanzar da zaman lafiya.

Shi ma a nasa jawabin Fasto Alhamdu John wanda ya zo daga Babban Birnin Tarayya Abuja ya bayyana jin dadinsa bisa samun ganawa da Khalifa Sanusi, inda ya kara da cewa, manufar ziyarar ita ce don a kara karfafa dankon zmunci da hadin kai.

Shi kuwa Fasto George Joshua daga jihar Biniwe, da yake yin tsokaci a kan gudunmawar da Khalifa ke ci gaba da bayarwa a matsayinsa na mabiyin darikar sugaye ta Tijanniyah, ya jaddada mahimmancin ganin mabiya Musulunci da Kirista na yin aiki da koyar da addinansu domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya, kauna da kuma hadin kai.

A nasa bangaren, Khalifa Sanusi Lamido ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ziyarar tare da yaba wa malaman addinin a kan tasu gudunmwar da wajen wanzar da zaman lafiya, musamman a Arewacin kasar nan.

Khalifa ya yi nuni da cewa, wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma aiki ne da ya rataya a kan kowanne dan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
uba sani

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa'i Sun Jahilci Aikin Majalisa - Barista Bello

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.