• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

by Abubakar Abba
1 year ago
in Labarai
0
Sanusi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Malaman addinin Kirista da suka fito daga Arewacin Nijeriya sun kai wa Sarkin Kano na 14 kuma Khalifan Tijjaniyya a Nijeriya, Sanusi Lamido Sanusi ziyarar ban girma a gidansa da ke jihar Kaduna.

Malaman sun kai ziyarar ce da nufin kara karfafa wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiya addinin Musulunci da na Kirista.

  • Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
  • Yadda CBN Ya Karya Darajar Naira – Sanusi

Babban Limanin Cocin Christ Ebangelical and Life Interbention Ministry da ke a Jihar Kaduna, Dakta Yohanna Buru ne ya jagoranci tawagar. Haka zalika, sun kai ziyarar ce domin jaddada muhimmancin martaba addinan juna da kara hadin kai a tsakanin mabiya addinai.

A jawabinsa, Buru ya jinjina wa Khalifa musamman a kan irin gudunmawar da yake ci gaba da bayarwa na wanzar da zaman lafiya don ci gaban kasar nan.

A cewar sa, Khalifa ya jima yana dabbaka wanzar da zaman lafiya da yada girmama addinan biyu da shigewa kan gaba wajen tattanawa ko yin muhara a kan zaman lafiya ba a Nijeriya kawai ba, har ma a daukacin fadin Nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Tawagar ta kuma yaba masa a kan namijin kokarin da yake ci gaba da yi, na yada zaman lafiya, mussamman kan gudunmawar da ya bayar na lalubo da mafita kan takaddamar kungiyar ECOWAS biyo bayan kifar da gwamnatin farar hula da sojin jamhuriyar Nijar suka yi a watannin baya, wanda suka yi nuni da cewa, wannan kokarin nasa ya cancanci a karrama shi da babbar lambar yabo ta duniya ta wanzar da zaman lafiya.

Shi ma a nasa jawabin Fasto Alhamdu John wanda ya zo daga Babban Birnin Tarayya Abuja ya bayyana jin dadinsa bisa samun ganawa da Khalifa Sanusi, inda ya kara da cewa, manufar ziyarar ita ce don a kara karfafa dankon zmunci da hadin kai.

Shi kuwa Fasto George Joshua daga jihar Biniwe, da yake yin tsokaci a kan gudunmawar da Khalifa ke ci gaba da bayarwa a matsayinsa na mabiyin darikar sugaye ta Tijanniyah, ya jaddada mahimmancin ganin mabiya Musulunci da Kirista na yin aiki da koyar da addinansu domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya, kauna da kuma hadin kai.

A nasa bangaren, Khalifa Sanusi Lamido ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ziyarar tare da yaba wa malaman addinin a kan tasu gudunmwar da wajen wanzar da zaman lafiya, musamman a Arewacin kasar nan.

Khalifa ya yi nuni da cewa, wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma aiki ne da ya rataya a kan kowanne dan kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken

Next Post

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa’i Sun Jahilci Aikin Majalisa – Barista Bello

Related

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

23 minutes ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

14 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

15 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

16 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

17 hours ago
Next Post
uba sani

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa'i Sun Jahilci Aikin Majalisa - Barista Bello

LABARAI MASU NASABA

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.