• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

by Abubakar Abba
1 year ago
in Labarai
0
Sanusi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Malaman addinin Kirista da suka fito daga Arewacin Nijeriya sun kai wa Sarkin Kano na 14 kuma Khalifan Tijjaniyya a Nijeriya, Sanusi Lamido Sanusi ziyarar ban girma a gidansa da ke jihar Kaduna.

Malaman sun kai ziyarar ce da nufin kara karfafa wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiya addinin Musulunci da na Kirista.

  • Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
  • Yadda CBN Ya Karya Darajar Naira – Sanusi

Babban Limanin Cocin Christ Ebangelical and Life Interbention Ministry da ke a Jihar Kaduna, Dakta Yohanna Buru ne ya jagoranci tawagar. Haka zalika, sun kai ziyarar ce domin jaddada muhimmancin martaba addinan juna da kara hadin kai a tsakanin mabiya addinai.

A jawabinsa, Buru ya jinjina wa Khalifa musamman a kan irin gudunmawar da yake ci gaba da bayarwa na wanzar da zaman lafiya don ci gaban kasar nan.

A cewar sa, Khalifa ya jima yana dabbaka wanzar da zaman lafiya da yada girmama addinan biyu da shigewa kan gaba wajen tattanawa ko yin muhara a kan zaman lafiya ba a Nijeriya kawai ba, har ma a daukacin fadin Nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Tawagar ta kuma yaba masa a kan namijin kokarin da yake ci gaba da yi, na yada zaman lafiya, mussamman kan gudunmawar da ya bayar na lalubo da mafita kan takaddamar kungiyar ECOWAS biyo bayan kifar da gwamnatin farar hula da sojin jamhuriyar Nijar suka yi a watannin baya, wanda suka yi nuni da cewa, wannan kokarin nasa ya cancanci a karrama shi da babbar lambar yabo ta duniya ta wanzar da zaman lafiya.

Shi ma a nasa jawabin Fasto Alhamdu John wanda ya zo daga Babban Birnin Tarayya Abuja ya bayyana jin dadinsa bisa samun ganawa da Khalifa Sanusi, inda ya kara da cewa, manufar ziyarar ita ce don a kara karfafa dankon zmunci da hadin kai.

Shi kuwa Fasto George Joshua daga jihar Biniwe, da yake yin tsokaci a kan gudunmawar da Khalifa ke ci gaba da bayarwa a matsayinsa na mabiyin darikar sugaye ta Tijanniyah, ya jaddada mahimmancin ganin mabiya Musulunci da Kirista na yin aiki da koyar da addinansu domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya, kauna da kuma hadin kai.

A nasa bangaren, Khalifa Sanusi Lamido ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ziyarar tare da yaba wa malaman addinin a kan tasu gudunmwar da wajen wanzar da zaman lafiya, musamman a Arewacin kasar nan.

Khalifa ya yi nuni da cewa, wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma aiki ne da ya rataya a kan kowanne dan kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken

Next Post

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa’i Sun Jahilci Aikin Majalisa – Barista Bello

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

42 minutes ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

3 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

7 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

9 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

9 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

10 hours ago
Next Post
uba sani

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa'i Sun Jahilci Aikin Majalisa - Barista Bello

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.