ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

by Abubakar Abba
2 years ago
Sanusi

Wasu Malaman addinin Kirista da suka fito daga Arewacin Nijeriya sun kai wa Sarkin Kano na 14 kuma Khalifan Tijjaniyya a Nijeriya, Sanusi Lamido Sanusi ziyarar ban girma a gidansa da ke jihar Kaduna.

Malaman sun kai ziyarar ce da nufin kara karfafa wanzar da zaman lafiya a tsakanin mabiya addinin Musulunci da na Kirista.

  • Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
  • Yadda CBN Ya Karya Darajar Naira – Sanusi

Babban Limanin Cocin Christ Ebangelical and Life Interbention Ministry da ke a Jihar Kaduna, Dakta Yohanna Buru ne ya jagoranci tawagar. Haka zalika, sun kai ziyarar ce domin jaddada muhimmancin martaba addinan juna da kara hadin kai a tsakanin mabiya addinai.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa, Buru ya jinjina wa Khalifa musamman a kan irin gudunmawar da yake ci gaba da bayarwa na wanzar da zaman lafiya don ci gaban kasar nan.

A cewar sa, Khalifa ya jima yana dabbaka wanzar da zaman lafiya da yada girmama addinan biyu da shigewa kan gaba wajen tattanawa ko yin muhara a kan zaman lafiya ba a Nijeriya kawai ba, har ma a daukacin fadin Nahiyar Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

Tawagar ta kuma yaba masa a kan namijin kokarin da yake ci gaba da yi, na yada zaman lafiya, mussamman kan gudunmawar da ya bayar na lalubo da mafita kan takaddamar kungiyar ECOWAS biyo bayan kifar da gwamnatin farar hula da sojin jamhuriyar Nijar suka yi a watannin baya, wanda suka yi nuni da cewa, wannan kokarin nasa ya cancanci a karrama shi da babbar lambar yabo ta duniya ta wanzar da zaman lafiya.

Shi ma a nasa jawabin Fasto Alhamdu John wanda ya zo daga Babban Birnin Tarayya Abuja ya bayyana jin dadinsa bisa samun ganawa da Khalifa Sanusi, inda ya kara da cewa, manufar ziyarar ita ce don a kara karfafa dankon zmunci da hadin kai.

Shi kuwa Fasto George Joshua daga jihar Biniwe, da yake yin tsokaci a kan gudunmawar da Khalifa ke ci gaba da bayarwa a matsayinsa na mabiyin darikar sugaye ta Tijanniyah, ya jaddada mahimmancin ganin mabiya Musulunci da Kirista na yin aiki da koyar da addinansu domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya, kauna da kuma hadin kai.

A nasa bangaren, Khalifa Sanusi Lamido ya bayyana jin dadinsa bisa wannan ziyarar tare da yaba wa malaman addinin a kan tasu gudunmwar da wajen wanzar da zaman lafiya, musamman a Arewacin kasar nan.

Khalifa ya yi nuni da cewa, wanzar da zaman lafiya a cikin al’umma aiki ne da ya rataya a kan kowanne dan kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
'yansanda
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista
Manyan Labarai

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Next Post
uba sani

Masu Zargin Uba Sani Kan Bashin el-Rufa'i Sun Jahilci Aikin Majalisa - Barista Bello

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025
Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

November 12, 2025
Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.