ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Sanusi

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Muhammad Sanusi, ya ce, a maimakon dora laifin halin kunci da matsatsi rayuwa da ake ciki a Nijeriya ga Shugaban kasa, Bola Tinubu, zarge-zargen da tuhume-tuhumen kai har ma da nuna yatsar, ya kamata ne a yi su kan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya bi wajen janyo matsaloli ga tattalin arziki.

Tsohon sarkin Kano, wanda ke jawabi ta tangaraho a ranar Lahadi a wajen wani taron addini da ya gudana a Abuja, ya ce tsohon gwamnatin da ta gabata ta kasa gudanar da tsare-tsaren da za su taimaka wa tattalin arziki.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

A cewarsa, Buhari ya toshe kunnuwansa kan yadda za a bi wajen magance matsalolin da suka shafi tattalin arzikin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, shi kam ba zai biye wa wasu gungun ‘yan Nijeriya da suke son ya soki Shugaban kasa Tinubu kan halin kunci da ake ciki a kasar nan ba.

Sanusi ya ce, “Tsawon shekaru na sha fada kan cewa za a fada matsalolin tattalin arziki. Dukkanin wani masanin tattalin arziki da ya fahimci yadda aka bi da tattalin arzikin kasar nan a shekaru takwas da suka wuce ya san za a iya tsintan kai cikin irin wannan mawuyacin yanayin.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

“Wannan kuncin rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta, yanzu ma aka fara shiga muddin ba a dauki matakan da suka dace ba, saboda Nijeriya ba ta kasance wata kasa ta daban ba, irin wannan yanayin ya faru a Jamus, Zimbabwe, Uganda, da Benezuela.

“Tsohon gwamnati ta toshe kunnuwarta ta ki sauraron rokonmu kan matakan da za a bi a kan tsarin tattalin arziki. Na fada a gaban shugaban kasan da ke mulki a yanzu a Jihar Kaduna, cewa duk wani dan siyasan da ya gaya muku cewa abubuwa za su yi sauki, kar ma ku zabeshi, saboda karya yake muku. Mutane sun yi watsi da shawarwarinmu ne da tunanin kawai maganace ake yi ta siyasa.

“Idan zan yi adalci ga Shugaba Bola Tinubu, ba shi ne ya dace a dora wa alhakin matsatsin da ake ciki ba a halin yanzu, sama da shekaru takwas muna rayuwa ciki tsari irin ta karya da lafto basuka daga kasashen waje da ya wuce hankali.

“Ba zan shiga a dama da ni ba wajen sukar Tinubu kan matsatsin rayuwa da ake fuskanta a yanzu ba, ba wai ina cewa shi din ba zai iya yin kuskure ba ne, amma a dai wannan matsatsin da ake ciki, shugaban kasa Tinubu bai da laifi. Zan yi magana muddin na ga wani kuskure a tsarin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu a nan gaba.” Sanusi ya shawarci masu hannu da shuni da su taimaka wa wadanda ba su da shi a halin da ake ciki tare da neman jama’a da su kara hakuri. Sannan, ya shawarci jama’a da su rage buri da dora wa kai abubuwan da ba su wajaba ba domin samun rayuwa cikin sauki da samun abincin da za a ci.

Sanusi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja
Labarai

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi
Labarai

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Next Post
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026
An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.