ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Sanusi

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Muhammad Sanusi, ya ce, a maimakon dora laifin halin kunci da matsatsi rayuwa da ake ciki a Nijeriya ga Shugaban kasa, Bola Tinubu, zarge-zargen da tuhume-tuhumen kai har ma da nuna yatsar, ya kamata ne a yi su kan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya bi wajen janyo matsaloli ga tattalin arziki.

Tsohon sarkin Kano, wanda ke jawabi ta tangaraho a ranar Lahadi a wajen wani taron addini da ya gudana a Abuja, ya ce tsohon gwamnatin da ta gabata ta kasa gudanar da tsare-tsaren da za su taimaka wa tattalin arziki.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

A cewarsa, Buhari ya toshe kunnuwansa kan yadda za a bi wajen magance matsalolin da suka shafi tattalin arzikin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, shi kam ba zai biye wa wasu gungun ‘yan Nijeriya da suke son ya soki Shugaban kasa Tinubu kan halin kunci da ake ciki a kasar nan ba.

Sanusi ya ce, “Tsawon shekaru na sha fada kan cewa za a fada matsalolin tattalin arziki. Dukkanin wani masanin tattalin arziki da ya fahimci yadda aka bi da tattalin arzikin kasar nan a shekaru takwas da suka wuce ya san za a iya tsintan kai cikin irin wannan mawuyacin yanayin.

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

“Wannan kuncin rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta, yanzu ma aka fara shiga muddin ba a dauki matakan da suka dace ba, saboda Nijeriya ba ta kasance wata kasa ta daban ba, irin wannan yanayin ya faru a Jamus, Zimbabwe, Uganda, da Benezuela.

“Tsohon gwamnati ta toshe kunnuwarta ta ki sauraron rokonmu kan matakan da za a bi a kan tsarin tattalin arziki. Na fada a gaban shugaban kasan da ke mulki a yanzu a Jihar Kaduna, cewa duk wani dan siyasan da ya gaya muku cewa abubuwa za su yi sauki, kar ma ku zabeshi, saboda karya yake muku. Mutane sun yi watsi da shawarwarinmu ne da tunanin kawai maganace ake yi ta siyasa.

“Idan zan yi adalci ga Shugaba Bola Tinubu, ba shi ne ya dace a dora wa alhakin matsatsin da ake ciki ba a halin yanzu, sama da shekaru takwas muna rayuwa ciki tsari irin ta karya da lafto basuka daga kasashen waje da ya wuce hankali.

“Ba zan shiga a dama da ni ba wajen sukar Tinubu kan matsatsin rayuwa da ake fuskanta a yanzu ba, ba wai ina cewa shi din ba zai iya yin kuskure ba ne, amma a dai wannan matsatsin da ake ciki, shugaban kasa Tinubu bai da laifi. Zan yi magana muddin na ga wani kuskure a tsarin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu a nan gaba.” Sanusi ya shawarci masu hannu da shuni da su taimaka wa wadanda ba su da shi a halin da ake ciki tare da neman jama’a da su kara hakuri. Sannan, ya shawarci jama’a da su rage buri da dora wa kai abubuwan da ba su wajaba ba domin samun rayuwa cikin sauki da samun abincin da za a ci.

Sanusi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Labarai

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.