• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara 2023: An Ƙaryata Jita-jitar Janyewar Takarar Dauda Lawal

byBello Hamza
3 years ago
dauda lawal

Ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na Dr. Dauda Lawal ya ƙaryata jita-jitar da ake yawo da ita na cewa yana shirin ficewa daga jam’iyyar PDP ya koma APC.

Dr. Dauda Lawal shi ne ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP.

 

  • Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa

A wata takardar sanarwar manema labarai da ofishin yaɗa labaran na Dauda Lawal ya fitar yau Asabar a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara ya ambaci wannan labari da shiryayyen ƙarya domin a ɓata sunan Dauda Lawal ɗin.

Ofishin ya ce, ba gaskiya ba ne batun cewa Dauda Lawal ya yi wata tattauna ta sirri da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Sani Yarima.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna kira ga dukkanin magoya bayan Gamjin Gusau, Dr. Dauda Lawal, ‘ya’yan jam’iyyar PDP da ma al’ummar Jihar Zamfara gabaɗaya da su yi watsi da wata jita-jita da ‘yan adawa suke yawo da ita.

“Jita-jitar tasu ta fi kama da wasan yara, saboda suna yawo da ƙaryar wai ɗan takarar Gwamna mai farin jini a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dauda Lawal zai koma APC.

“Wannan lamari bai bamu mamaki ba, saboda mun san jam’iyya mai mulki ba ta da wani abin arziki da za ta iya yin farfaganda da shi, sai dai su dogara da ƙarairayi da sharri don ganin sun dushe hasken Gamjin Gusau.

“Tun bayan da Dauda Lawal ya ayyana aniyarsa ta yin takara suka shiga cikin ruɗani da fargaba. Bayan da ya lashe zaɓen fidda gwanin PDP na Jihar Zamfara, sai hankulansu suka tashi, suka shiga neman hanyoyin yaɗa sharri.

“Ai abu ne ma da hankali ba zai ɗauka ba, a ce mutumin da aka zaɓa a matsayin ɗan takarar gwamna a wata jam’iyya daban ya ajiye takara ya sauya sheƙa. Wannan irin farfaganda ko ƙananan yara ba za su yarda da ita ba. Ko ba komi wannan alamu ne na nasara, cewa jam’iyya mai mulki ta fahimci lokaci ya ƙure mata, kuma tauraron Dauda Lawal ne ke haskawa yanzu a Zamfara.

 

  • https://leadership.ng/12-quick-facts-about-zamfara-pdp-candidate-dr-dauda-lawal/

“Muna yin amfani da wannan dama wurin sanar da al’umma cewa, duk wata sanarwa da ba ta fito kaitsaye daga wurin ɗan takarar gwamna, Dr. Dauda Lawal ko ofishin yaɗa labaransa ba, a yi watsi da ita.” Inji ofishin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version