ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara 2023: An Ƙaryata Jita-jitar Janyewar Takarar Dauda Lawal

by Bello Hamza
4 years ago
dauda lawal

Ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na Dr. Dauda Lawal ya ƙaryata jita-jitar da ake yawo da ita na cewa yana shirin ficewa daga jam’iyyar PDP ya koma APC.

Dr. Dauda Lawal shi ne ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP.

 

ADVERTISEMENT
  • Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa

A wata takardar sanarwar manema labarai da ofishin yaɗa labaran na Dauda Lawal ya fitar yau Asabar a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara ya ambaci wannan labari da shiryayyen ƙarya domin a ɓata sunan Dauda Lawal ɗin.

Ofishin ya ce, ba gaskiya ba ne batun cewa Dauda Lawal ya yi wata tattauna ta sirri da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Sani Yarima.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna kira ga dukkanin magoya bayan Gamjin Gusau, Dr. Dauda Lawal, ‘ya’yan jam’iyyar PDP da ma al’ummar Jihar Zamfara gabaɗaya da su yi watsi da wata jita-jita da ‘yan adawa suke yawo da ita.

“Jita-jitar tasu ta fi kama da wasan yara, saboda suna yawo da ƙaryar wai ɗan takarar Gwamna mai farin jini a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dauda Lawal zai koma APC.

“Wannan lamari bai bamu mamaki ba, saboda mun san jam’iyya mai mulki ba ta da wani abin arziki da za ta iya yin farfaganda da shi, sai dai su dogara da ƙarairayi da sharri don ganin sun dushe hasken Gamjin Gusau.

“Tun bayan da Dauda Lawal ya ayyana aniyarsa ta yin takara suka shiga cikin ruɗani da fargaba. Bayan da ya lashe zaɓen fidda gwanin PDP na Jihar Zamfara, sai hankulansu suka tashi, suka shiga neman hanyoyin yaɗa sharri.

“Ai abu ne ma da hankali ba zai ɗauka ba, a ce mutumin da aka zaɓa a matsayin ɗan takarar gwamna a wata jam’iyya daban ya ajiye takara ya sauya sheƙa. Wannan irin farfaganda ko ƙananan yara ba za su yarda da ita ba. Ko ba komi wannan alamu ne na nasara, cewa jam’iyya mai mulki ta fahimci lokaci ya ƙure mata, kuma tauraron Dauda Lawal ne ke haskawa yanzu a Zamfara.

 

  • https://leadership.ng/12-quick-facts-about-zamfara-pdp-candidate-dr-dauda-lawal/

“Muna yin amfani da wannan dama wurin sanar da al’umma cewa, duk wata sanarwa da ba ta fito kaitsaye daga wurin ɗan takarar gwamna, Dr. Dauda Lawal ko ofishin yaɗa labaransa ba, a yi watsi da ita.” Inji ofishin.

dauda lawal
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.