ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara 2023: An Ƙaryata Jita-jitar Janyewar Takarar Dauda Lawal

by Bello Hamza
4 years ago
dauda lawal

Ofishin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na Dr. Dauda Lawal ya ƙaryata jita-jitar da ake yawo da ita na cewa yana shirin ficewa daga jam’iyyar PDP ya koma APC.

Dr. Dauda Lawal shi ne ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP.

 

ADVERTISEMENT
  • Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa

A wata takardar sanarwar manema labarai da ofishin yaɗa labaran na Dauda Lawal ya fitar yau Asabar a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara ya ambaci wannan labari da shiryayyen ƙarya domin a ɓata sunan Dauda Lawal ɗin.

Ofishin ya ce, ba gaskiya ba ne batun cewa Dauda Lawal ya yi wata tattauna ta sirri da tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Sani Yarima.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna kira ga dukkanin magoya bayan Gamjin Gusau, Dr. Dauda Lawal, ‘ya’yan jam’iyyar PDP da ma al’ummar Jihar Zamfara gabaɗaya da su yi watsi da wata jita-jita da ‘yan adawa suke yawo da ita.

“Jita-jitar tasu ta fi kama da wasan yara, saboda suna yawo da ƙaryar wai ɗan takarar Gwamna mai farin jini a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dauda Lawal zai koma APC.

“Wannan lamari bai bamu mamaki ba, saboda mun san jam’iyya mai mulki ba ta da wani abin arziki da za ta iya yin farfaganda da shi, sai dai su dogara da ƙarairayi da sharri don ganin sun dushe hasken Gamjin Gusau.

“Tun bayan da Dauda Lawal ya ayyana aniyarsa ta yin takara suka shiga cikin ruɗani da fargaba. Bayan da ya lashe zaɓen fidda gwanin PDP na Jihar Zamfara, sai hankulansu suka tashi, suka shiga neman hanyoyin yaɗa sharri.

“Ai abu ne ma da hankali ba zai ɗauka ba, a ce mutumin da aka zaɓa a matsayin ɗan takarar gwamna a wata jam’iyya daban ya ajiye takara ya sauya sheƙa. Wannan irin farfaganda ko ƙananan yara ba za su yarda da ita ba. Ko ba komi wannan alamu ne na nasara, cewa jam’iyya mai mulki ta fahimci lokaci ya ƙure mata, kuma tauraron Dauda Lawal ne ke haskawa yanzu a Zamfara.

 

  • https://leadership.ng/12-quick-facts-about-zamfara-pdp-candidate-dr-dauda-lawal/

“Muna yin amfani da wannan dama wurin sanar da al’umma cewa, duk wata sanarwa da ba ta fito kaitsaye daga wurin ɗan takarar gwamna, Dr. Dauda Lawal ko ofishin yaɗa labaransa ba, a yi watsi da ita.” Inji ofishin.

dauda lawal
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

Dabbobi 5 Da Ake Samun Riba Mai Yawo A Kiwonsu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.