• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana cewa Jihar Zamfara na cin gajiyar tsananin hasken rana a duk shekara, inda ya sanya ta a matsayin wurin da ya dace da gonaki masu amfani da hasken rana da na’urorin samar da wutar lantarki masu zaman kansu.

 

Hukumar Raya Wutar Lantarki ta Karkara (REA) ta gudanar da taron tattaunawa da masana na jihar Zamfara a ranar Larabar da ta gabata a Abuja, inda ta tattaro masu ruwa da tsaki a fannin lantarki a ci gaba da tarukan dabarunta na jiha zuwa jiha.

  • Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa taron ya mayar da hankali ne kan farfaɗo da harkar wutar lantarki ta Zamfara, domin inganta zamantakewar al’umma, da ci gaba, da ƙirƙire-ƙirƙire ta hanyar samar da tsayayyen lantarki.

 

Labarai Masu Nasaba

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Sanarwar ta ƙara da cewa, a yayin taron an sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Hukumar Samar da Wutar Lantarki ta Yankunan Karkara, sannan aka tattauna da masu ruwa da tsaki, tambayoyi da amsoshi, ra’ayoyi, da kuma alƙawura.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce ya gaji matalauciyar gwamnatin a bangaten lantarki.

 

Ya ci gaba da cewa, “An katse ƙananan hukumomi da yawa daga babban lantarkin ƙasa. An sace wayoyin lantarki da dama, wasu kuma sun lalace, wasu muhimman ababen more rayuwa sun durƙushe a cikin shekaru saboda watsi da su, sannan masana’antu da kasuwancinmu sun gurgunta saboda rashin ingantaccen wutar lantarki.

 

“Duk da haka, mun zaɓi kada mu shiga wasan zargi, a maimakon haka, mun mayar da martani ga ƙalubalen da muka gamu da su tare da hangen nesa mai muhimmanci, ƙuduri aiwatar da aiki da kuma yanke hukuncin cikin gaggawa.

 

“Tun daga wannan lokacin ne gwamnatinmu ta fara aikin sake rubuta wannan labari ta hanyar sanya hanyoyin samar da wutar lantarki a cikin dabarun ci gabanmu, mun ƙaddamar da ɗaya daga cikin shirye-shiryen samar da taransfoma na ƙasar nan, inda muka tura taransifoma sama da guda 150 a cikin birane da ƙauyuka.

 

“A tare da haɗin gwiwar Kamfanin Samar da Wutar Lantarki ta Kaduna mun maido da wutar lantarki a ƙananan hukumomi shida, kuma mun sake haxe wasu guda bakwai, waɗanda wasu daga cikinsu ba su da wutar lantarki sama da shekaru goma, wannan ƙoƙari na cikin wani shiri na zaburar da masana’antu, da kuma buɗe kasuwanni masu zaman kansu.

 

Gwamna Lawal ya ce, Zamfara tana ba da damammaki masu kyau don saka hannun jari a bangaren lantarki. “An albarkace mu da hasken rana mai tsananin ƙarfi a duk shekara, wanda ya sa mu zama wuri na farko da gonakin hasken rana za su samu habaka cikin sauri.

 

“Idan aka duba za a babban damar da madatsar ruwa ta Bakalori ke da shi, kadara ce ta samar da wutar lantarki da ba a yi amfani da ita ba, tare da yanki sama da hekta 30,000 na ban ruwa. Wannan haɗin gwiwa na hasken rana yana ba da damar ƙaddamar da hanyoyin samar da lantarki wanda zai iya ci gaba da ƙarfafa birane da karkara.

 

“Bangaren nomanmu wani muhimmin batu ne, a kullum jihar Zamfara tana cikin jerin manyan jihohin da ke girbin gero, dawa, waken soya, da gyaɗa a Nijeriya, muna sake fasalin wannan fanni ta hanyar ingantattun kayan aiki, injininan noma na zamani, da gyaran ban ruwa.

 

“Babban misalin sabunta kayan aikin mu shi ne filin jirgin sama na Gusau da filin jirageb ɗaukar kaya da ke kusa da shi, wanda aka tsara shi a matsayin ƙofa ga fasinjoji, kasuwanci da saka hannun jari.

 

“Don cimma burinmu na noma, muna nufin wannan ginin ya zama filin jirgin sama na farko a Nujeriya wanda zai samu wutar lantarki aƙalla kashi 50 cikin 100, kuma zai bai wa RESCO damar jagorantar sufurin jiragen sama mai ɗorewa.”

 

Tun da farko, Manajan Daraktan REA, Abba Abubakar Aliyu, ya tabbatar wa Gwamna Lawal ƙudirin hukumar na samar da kayayyakin wutar lantarki a jihar Zamfara.

 

“A karon farko a tarihin Nijeriya an yi taswirar ƙasar baki ɗaya, kuma hakan ya nuna adadin mutanen da ba su da wutar lantarki da kuma wurin da suke da shi, yanayin al’ummarsu da kuma buƙatar wutar lantarki, hakan ya taimaka wa RESCO da kuɗi, kuma gwamnatin jihar ta samu dabarar da za a bi don ganin cewa waɗannan mutanen sun samu wutar lantarki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

Next Post

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Related

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

7 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

8 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

9 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

10 hours ago
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

13 hours ago
Next Post
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.