• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Shirya Wa Kiwo, In Ji Ministan Bunkasa Kiwon Dabbobi

by Sulaiman
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Zamfara Ta Shirya Wa Kiwo, In Ji Ministan Bunkasa Kiwon Dabbobi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya tabbatar wa Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon Dabbobi cewa jihar Zamfara na da wuraren da za a yi kiwo.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ziyarci hedikwatar ma’aikatar a wata ziyarar ban girma da ya kai wa ministan, Alhaji Idi Mukhtar Maiha.

  • Hukumar JAMB Ta Zuba Naira Biliyan 6 A Asusun Gwamnatin Tarayya A Shekarar 2024
  • Da Ɗumi-Ɗumi: Babban Layin Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Karon Farko A 2025

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, jihar Zamfara, kasancewarta jihar noma da kiwo tana taka rawar gani a aikin ma’aikatar binƙasa kiwon dabbobi.

 

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Sanarwar ta ƙara da cewa, an ƙirƙiro ma’aikatar ne a watan Yulin 2024 domin gyara masana’antar kiwon dabbobin Nijeriya, da samar da yanayi mai inganci, da ƙarfafa zuba jari na cikin gida da na ƙasashen waje, da kuma inganta samar da abinci.

 

A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya bayyana aniyar gwamnatinsa na haɗa kai wajen lalubo baiwar da jihar Zamfara ke da shi.

 

“Minista, kamar yadda ka sani, Zamfara al’umma ce ta noma. Shi ya sa taken mu shi ne, ‘Noma Abin Alfaharinmu Ne’.

 

“Mun zo nan ne a yau domin taya ku murna da kafa wannan sabuwar ma’aikatar, wadda nake da yaƙinin ta dace. Bugu da ƙari, muna da burin samar da haɗin gwiwa mai ƙarfi tsakanin jihar mu da ma’aikatar.

 

“A Zamfara, madatsun ruwa da dama a faɗin jihar na buƙatar gyara don samar wa dabbobi da ruwa, haka kuma za a iya samun damar ɗaukar duk wani shiri.

 

“Muna gayyatar Minista da tawagarsa da su ziyarci Zamfara domin duba yanayin kiwo na jihar.”

 

A lokacin da yake mayar da martani, ministan harkokin kiwo, Idi Mukhtar Maiha, ya gode wa gwamna Lawal bisa ziyarar da ya kai ma’aikatar.

 

“Tun da aka kafa ma’aikatar, ba mu samu ziyarar wani gwamna mai zartarwa da ke da buƙatar jin abin da za mu iya bayarwa ba.

 

“Ina so in tabbatar muku cewa a shirye muke mu ba ku haɗin kai don kawo sauyi da magance matsalolin ku a fannin kiwon dabbobi a Zamfara.

 

“Bangaren kiwo ya daɗe yana aiki ba bisa ƙa’ida ba. Za mu zamanantar da wannan fanni ta hanyar tsare-tsare daban-daban.

 

“Gwamna, jihar Zamfara ce za ta zama jihar da za ta yi gwaji domin nuna ajandar sabuwar ma’aikatar. Da wannan haɗin gwiwa za mu mayar da Gidan Jaji da ke Zamfara wata ƙaramar cibiyar kiwo,” inji ministan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Next Post

Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

13 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

16 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

1 day ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

1 day ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

2 days ago
Next Post
Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi

Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi

LABARAI MASU NASABA

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.