• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Shirya Wa Kiwo, In Ji Ministan Bunkasa Kiwon Dabbobi

by Sulaiman
10 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya tabbatar wa Ma’aikatar Bunƙasa Kiwon Dabbobi cewa jihar Zamfara na da wuraren da za a yi kiwo.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ziyarci hedikwatar ma’aikatar a wata ziyarar ban girma da ya kai wa ministan, Alhaji Idi Mukhtar Maiha.

  • Hukumar JAMB Ta Zuba Naira Biliyan 6 A Asusun Gwamnatin Tarayya A Shekarar 2024
  • Da Ɗumi-Ɗumi: Babban Layin Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Karon Farko A 2025

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa, jihar Zamfara, kasancewarta jihar noma da kiwo tana taka rawar gani a aikin ma’aikatar binƙasa kiwon dabbobi.

 

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, an ƙirƙiro ma’aikatar ne a watan Yulin 2024 domin gyara masana’antar kiwon dabbobin Nijeriya, da samar da yanayi mai inganci, da ƙarfafa zuba jari na cikin gida da na ƙasashen waje, da kuma inganta samar da abinci.

 

A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya bayyana aniyar gwamnatinsa na haɗa kai wajen lalubo baiwar da jihar Zamfara ke da shi.

 

“Minista, kamar yadda ka sani, Zamfara al’umma ce ta noma. Shi ya sa taken mu shi ne, ‘Noma Abin Alfaharinmu Ne’.

 

“Mun zo nan ne a yau domin taya ku murna da kafa wannan sabuwar ma’aikatar, wadda nake da yaƙinin ta dace. Bugu da ƙari, muna da burin samar da haɗin gwiwa mai ƙarfi tsakanin jihar mu da ma’aikatar.

 

“A Zamfara, madatsun ruwa da dama a faɗin jihar na buƙatar gyara don samar wa dabbobi da ruwa, haka kuma za a iya samun damar ɗaukar duk wani shiri.

 

“Muna gayyatar Minista da tawagarsa da su ziyarci Zamfara domin duba yanayin kiwo na jihar.”

 

A lokacin da yake mayar da martani, ministan harkokin kiwo, Idi Mukhtar Maiha, ya gode wa gwamna Lawal bisa ziyarar da ya kai ma’aikatar.

 

“Tun da aka kafa ma’aikatar, ba mu samu ziyarar wani gwamna mai zartarwa da ke da buƙatar jin abin da za mu iya bayarwa ba.

 

“Ina so in tabbatar muku cewa a shirye muke mu ba ku haɗin kai don kawo sauyi da magance matsalolin ku a fannin kiwon dabbobi a Zamfara.

 

“Bangaren kiwo ya daɗe yana aiki ba bisa ƙa’ida ba. Za mu zamanantar da wannan fanni ta hanyar tsare-tsare daban-daban.

 

“Gwamna, jihar Zamfara ce za ta zama jihar da za ta yi gwaji domin nuna ajandar sabuwar ma’aikatar. Da wannan haɗin gwiwa za mu mayar da Gidan Jaji da ke Zamfara wata ƙaramar cibiyar kiwo,” inji ministan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
Manyan Labarai

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Next Post
Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi

Rahoto Ya Nuna Yadda Kanana Da Matsakaitan Kamfanonin Sin Ke Tafiya Cikin Tagomashi

LABARAI MASU NASABA

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.