• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Kano

Sabon Darakta Janar na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Ahmed Musa, ya bayyana cewa samun mukamin shugabanci a ƙungiyar ba zai hana shi ci gaba da taka leda ba. A wata hira da yayi da RFI Hausa, Musa ya bayyana cewa kasancewarsa tsohon ɗan wasan Pillars tun lokacin ƙuruciya ne ya sanya zuciyarsa ke cike da ƙauna da kishin ƙungiyar. Ya ce yana jin ciwo idan ƙungiyar ta shiga halin rashin nasara, don haka zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa.

Ahmed Musa ya kuma jaddada buƙatar samun cikakken goyon bayan magoya bayan Kano Pillars domin a samu damar farfaɗo da martabar ƙungiyar a fagen ƙwallon ƙafa. A cewarsa, ƙungiyar na buƙatar haɗin kai da jajircewar kowa domin samun nasara, musamman a wannan sabon zamani da ƙwallon ƙafa ke ƙara fuskantar ƙalubale.

  • Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

A cikin kwanakin baya, Ahmed Musa ya jagoranci ƙulla yarjejeniya da RFI Hausa, wadda ya ce ita ce irinta ta farko da ƙungiyar ta taɓa samu tun kafuwarta. Yarjejeniyar ta kunshi samar da kayan wasanni da kuma kayayyakin aikin sada zumunta (Social Media), wanda zai ƙara inganta ayyukan ƙungiyar da kuma hulɗarta da duniya ta zamani.

Musa ya ce kasancewarsa a matsayin Manajan ƙungiyar ba zai hana shi taka leda ba idan buƙatar hakan ta taso. Ya bayyana cewa duk lokacin da ya ke wajen aiki, Ciyaman na ƙungiyar zai ci gaba da kula da duk wasu al’amuran ofishin ba tare da tangarɗa ba. Wannan, a cewarsa, zai tabbatar da cewa shugabancin ƙungiyar bai tsaya ga mutum ɗaya ba.

A ƙarshe, Ahmed Musa ya buƙaci gwamnatin jihar Kano da ta ƙara zage damtse wajen tallafa wa ƙungiyar da kayan aiki da kuɗi. Ya ce burinsu shi ne su mayar da Pillars ƙungiyar da za a riƙa tsoro a gasar ƙwallon ƙafa a Nijeriya, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan an samu cikakken tallafi daga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

LABARAI MASU NASABA

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu
Manyan Labarai

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Kano

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.