• English
  • Business News
Thursday, July 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

by Abubakar Sulaiman
7 hours ago
in Wasanni
0
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Darakta Janar na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Ahmed Musa, ya bayyana cewa samun mukamin shugabanci a ƙungiyar ba zai hana shi ci gaba da taka leda ba. A wata hira da yayi da RFI Hausa, Musa ya bayyana cewa kasancewarsa tsohon ɗan wasan Pillars tun lokacin ƙuruciya ne ya sanya zuciyarsa ke cike da ƙauna da kishin ƙungiyar. Ya ce yana jin ciwo idan ƙungiyar ta shiga halin rashin nasara, don haka zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa.

Ahmed Musa ya kuma jaddada buƙatar samun cikakken goyon bayan magoya bayan Kano Pillars domin a samu damar farfaɗo da martabar ƙungiyar a fagen ƙwallon ƙafa. A cewarsa, ƙungiyar na buƙatar haɗin kai da jajircewar kowa domin samun nasara, musamman a wannan sabon zamani da ƙwallon ƙafa ke ƙara fuskantar ƙalubale.

  • Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

A cikin kwanakin baya, Ahmed Musa ya jagoranci ƙulla yarjejeniya da RFI Hausa, wadda ya ce ita ce irinta ta farko da ƙungiyar ta taɓa samu tun kafuwarta. Yarjejeniyar ta kunshi samar da kayan wasanni da kuma kayayyakin aikin sada zumunta (Social Media), wanda zai ƙara inganta ayyukan ƙungiyar da kuma hulɗarta da duniya ta zamani.

Musa ya ce kasancewarsa a matsayin Manajan ƙungiyar ba zai hana shi taka leda ba idan buƙatar hakan ta taso. Ya bayyana cewa duk lokacin da ya ke wajen aiki, Ciyaman na ƙungiyar zai ci gaba da kula da duk wasu al’amuran ofishin ba tare da tangarɗa ba. Wannan, a cewarsa, zai tabbatar da cewa shugabancin ƙungiyar bai tsaya ga mutum ɗaya ba.

A ƙarshe, Ahmed Musa ya buƙaci gwamnatin jihar Kano da ta ƙara zage damtse wajen tallafa wa ƙungiyar da kayan aiki da kuɗi. Ya ce burinsu shi ne su mayar da Pillars ƙungiyar da za a riƙa tsoro a gasar ƙwallon ƙafa a Nijeriya, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan an samu cikakken tallafi daga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoPillars
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Next Post

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

1 day ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

2 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

3 days ago
Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

4 days ago
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain
Wasanni

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

5 days ago
Next Post
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

July 23, 2025
An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

July 23, 2025
Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

July 23, 2025
Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

July 23, 2025
Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

July 23, 2025
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

July 23, 2025
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

July 23, 2025
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.