• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Goyi Bayan Peter Obi A 2027 Matsawar PDP Ta Sahale Masa Yin Takara – Atiku

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Muƙala, Siyasa
0
Zan Goyi Bayan Peter Obi A 2027 Matsawar PDP Ta Sahale Masa Yin Takara – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyun adawa a Nijeriya na wani shirin ƙarƙashin ƙasa don kawar da jam’iyyar APC mai mulki a kakar zaɓe me zuwa ta 2027.

Wanda muryarsa ta fi amo cikin masu wannan buri na ganin an yi haɗakar shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, wanda tun bayan da ya gaza kai labari a sakamakon ɓarakar da jam’iyyarsa ta PDP ta samu ya gano cewa lallai shi kaɗai ko PDP kaɗai ba za su iya kayar da APC.

  • Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido
  • 2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

Bayan haka Wazirin Adamawan Atiku Abubakar wanda ya yi wa jam’iyyar PDP takarar shugabancin ƙasa a zaben 2023, na da cikakkiyar masaniyar yadda haɗaka ke tasiri wajen yin nasarar zaɓe domin ita suka yi a baya suka kayar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan.

Don haka ne ma bayan da suka kaye a hannun shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya duƙufa ainun wajen miƙa ƙoƙon barar a yi haɗaka tsakanin manyan jam’iyyun hamayya irinsu Labour (Party Peter Obi) da NNPP (Rabi’u Kwankwaso).

Ana kyautata zaton dai a kan wannan gaɓa ce ta haɗin kai Peter Obi ya kai wa Waziri Atiku ziyara, domin ya an jiyo Atikun yana cewa; “Ga duk wanda ya ke gani za a samu wani rikici tsakanina da Obi to babu abin da zai faru ko kadan, kuma mu a nan gaba kowa a dauko don ya yi takara in dai ya cancanta zamu goyi bayansa.”

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Atikun dai ya bayyana cewa shi baya ƙin a samu shuagaban ƙasa daga kudu domin kuwa “Ai a baya na fada cewa idan jam’iyarmu zamu hadu ace a bar wa mutumin da ya fito daga Kudu maso Gabas zamu yar da.”

Wanda hakan ke nufin ko da Peter Obi PDP ta tsayar Atikun zai mara masa baya, sai kuma hakan da kamar wuya domin yanzu mulki na kudu nan gaba kenna Arewa zai dawo. Da kamar wuya a sake tsayar da ɗan kudun takara.

Yanzu dai tattaunawa ta fara ɗauka harama musamman tsakanin Labour Party da PDP sai dai har yanzu babu wani takamaiman bayani daga tsagin NNPP duk kuwa da a baya an ji yo Rabi’u Musa Kwankwaso yana cewa ƙofarsu a buɗe take don a kafa jam’iyyar haɗaka.

Daga cikin abin da zai ba wa PDP wahala shi ne shawo kan Kwankwaso ya yarda a haɗe da PDP, domin a burin Kwankwaso sai dai ko a dawo NNPP ko kuma a kafa sabuwar jam’iyya ba wai su sake komawa PDP ba.

Wazirin Adamawa din ya ce ba zai yi ritaya daga harkokin siyasa ba kuma za a ci gaba da dama wa da shi har sai lokacin da rai ya yi halinsa.

Batun takararsa kuwa Atiku Abubakar, ya ce,” A yanzu sai a saurara zuwa 2027 a gani ko zan tsaya takara ko kuma a’a.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027AtikuAtiku AbubakarElectionPeter ObiPolitics
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Next Post

Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

Related

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

1 day ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

3 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

3 days ago
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

4 days ago
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
Siyasa

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

4 days ago
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano
Siyasa

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

6 days ago
Next Post
Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.