• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Goyi Bayan Peter Obi A 2027 Matsawar PDP Ta Sahale Masa Yin Takara – Atiku

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Muƙala, Siyasa
0
Zan Goyi Bayan Peter Obi A 2027 Matsawar PDP Ta Sahale Masa Yin Takara – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyun adawa a Nijeriya na wani shirin ƙarƙashin ƙasa don kawar da jam’iyyar APC mai mulki a kakar zaɓe me zuwa ta 2027.

Wanda muryarsa ta fi amo cikin masu wannan buri na ganin an yi haɗakar shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, wanda tun bayan da ya gaza kai labari a sakamakon ɓarakar da jam’iyyarsa ta PDP ta samu ya gano cewa lallai shi kaɗai ko PDP kaɗai ba za su iya kayar da APC.

  • Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido
  • 2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

Bayan haka Wazirin Adamawan Atiku Abubakar wanda ya yi wa jam’iyyar PDP takarar shugabancin ƙasa a zaben 2023, na da cikakkiyar masaniyar yadda haɗaka ke tasiri wajen yin nasarar zaɓe domin ita suka yi a baya suka kayar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan.

Don haka ne ma bayan da suka kaye a hannun shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya duƙufa ainun wajen miƙa ƙoƙon barar a yi haɗaka tsakanin manyan jam’iyyun hamayya irinsu Labour (Party Peter Obi) da NNPP (Rabi’u Kwankwaso).

Ana kyautata zaton dai a kan wannan gaɓa ce ta haɗin kai Peter Obi ya kai wa Waziri Atiku ziyara, domin ya an jiyo Atikun yana cewa; “Ga duk wanda ya ke gani za a samu wani rikici tsakanina da Obi to babu abin da zai faru ko kadan, kuma mu a nan gaba kowa a dauko don ya yi takara in dai ya cancanta zamu goyi bayansa.”

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Atikun dai ya bayyana cewa shi baya ƙin a samu shuagaban ƙasa daga kudu domin kuwa “Ai a baya na fada cewa idan jam’iyarmu zamu hadu ace a bar wa mutumin da ya fito daga Kudu maso Gabas zamu yar da.”

Wanda hakan ke nufin ko da Peter Obi PDP ta tsayar Atikun zai mara masa baya, sai kuma hakan da kamar wuya domin yanzu mulki na kudu nan gaba kenna Arewa zai dawo. Da kamar wuya a sake tsayar da ɗan kudun takara.

Yanzu dai tattaunawa ta fara ɗauka harama musamman tsakanin Labour Party da PDP sai dai har yanzu babu wani takamaiman bayani daga tsagin NNPP duk kuwa da a baya an ji yo Rabi’u Musa Kwankwaso yana cewa ƙofarsu a buɗe take don a kafa jam’iyyar haɗaka.

Daga cikin abin da zai ba wa PDP wahala shi ne shawo kan Kwankwaso ya yarda a haɗe da PDP, domin a burin Kwankwaso sai dai ko a dawo NNPP ko kuma a kafa sabuwar jam’iyya ba wai su sake komawa PDP ba.

Wazirin Adamawa din ya ce ba zai yi ritaya daga harkokin siyasa ba kuma za a ci gaba da dama wa da shi har sai lokacin da rai ya yi halinsa.

Batun takararsa kuwa Atiku Abubakar, ya ce,” A yanzu sai a saurara zuwa 2027 a gani ko zan tsaya takara ko kuma a’a.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027AtikuAtiku AbubakarElectionPeter ObiPolitics
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Firaministan Faransa: Duniya Na Hasashen Kyakkyawar Makoma Ga Kasar Sin

Next Post

Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

Related

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

1 hour ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

7 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
Next Post
Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.