• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Goyi Bayan Peter Obi A 2027 Matsawar PDP Ta Sahale Masa Yin Takara – Atiku

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Peter Obi

Jam’iyyun adawa a Nijeriya na wani shirin ƙarƙashin ƙasa don kawar da jam’iyyar APC mai mulki a kakar zaɓe me zuwa ta 2027.

Wanda muryarsa ta fi amo cikin masu wannan buri na ganin an yi haɗakar shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, wanda tun bayan da ya gaza kai labari a sakamakon ɓarakar da jam’iyyarsa ta PDP ta samu ya gano cewa lallai shi kaɗai ko PDP kaɗai ba za su iya kayar da APC.

  • Obi Na Jam’iyyar Labour Ya Yi Wata Ganawar Sirri Da Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamido
  • 2027: PDP Za Ta Yanke Hukunci Kan Makomata — Atiku

Bayan haka Wazirin Adamawan Atiku Abubakar wanda ya yi wa jam’iyyar PDP takarar shugabancin ƙasa a zaben 2023, na da cikakkiyar masaniyar yadda haɗaka ke tasiri wajen yin nasarar zaɓe domin ita suka yi a baya suka kayar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan.

Don haka ne ma bayan da suka kaye a hannun shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya duƙufa ainun wajen miƙa ƙoƙon barar a yi haɗaka tsakanin manyan jam’iyyun hamayya irinsu Labour (Party Peter Obi) da NNPP (Rabi’u Kwankwaso).

Ana kyautata zaton dai a kan wannan gaɓa ce ta haɗin kai Peter Obi ya kai wa Waziri Atiku ziyara, domin ya an jiyo Atikun yana cewa; “Ga duk wanda ya ke gani za a samu wani rikici tsakanina da Obi to babu abin da zai faru ko kadan, kuma mu a nan gaba kowa a dauko don ya yi takara in dai ya cancanta zamu goyi bayansa.”

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Atikun dai ya bayyana cewa shi baya ƙin a samu shuagaban ƙasa daga kudu domin kuwa “Ai a baya na fada cewa idan jam’iyarmu zamu hadu ace a bar wa mutumin da ya fito daga Kudu maso Gabas zamu yar da.”

Wanda hakan ke nufin ko da Peter Obi PDP ta tsayar Atikun zai mara masa baya, sai kuma hakan da kamar wuya domin yanzu mulki na kudu nan gaba kenna Arewa zai dawo. Da kamar wuya a sake tsayar da ɗan kudun takara.

Yanzu dai tattaunawa ta fara ɗauka harama musamman tsakanin Labour Party da PDP sai dai har yanzu babu wani takamaiman bayani daga tsagin NNPP duk kuwa da a baya an ji yo Rabi’u Musa Kwankwaso yana cewa ƙofarsu a buɗe take don a kafa jam’iyyar haɗaka.

Daga cikin abin da zai ba wa PDP wahala shi ne shawo kan Kwankwaso ya yarda a haɗe da PDP, domin a burin Kwankwaso sai dai ko a dawo NNPP ko kuma a kafa sabuwar jam’iyya ba wai su sake komawa PDP ba.

Wazirin Adamawa din ya ce ba zai yi ritaya daga harkokin siyasa ba kuma za a ci gaba da dama wa da shi har sai lokacin da rai ya yi halinsa.

Batun takararsa kuwa Atiku Abubakar, ya ce,” A yanzu sai a saurara zuwa 2027 a gani ko zan tsaya takara ko kuma a’a.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Peter Obi
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
Next Post
Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

Noman Aya Da Yadda Yake Samar Da Kudin Shiga

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.