• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

bySadiq
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce zai ware Dala biliyan 10 domin magance matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku ya bayyana hakan ne a Ilorin, babban birnin Jihar Kwara a wajen kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar PDP na Arewa ta Tsakiya, wanda aka gudanar a dandalin Ilorin.

  • Yadda ‘Yan Majalisa Suka Bai Wa Hammata Iska A Saliyo
  • Matsalar Karancin Man Fetur Na Ci Gaba Da Ta’azzara A Legas

Tsohon mataimakin shugaban kasar nan, ya ce za a yi amfani da kudin ne wajen taimaka wa matasan Nijeriya wajen kafa kanana da matsakaitan masana’antu.

“Ina so in tabbatar muku da cewa rashin aikin yi da matasa ke fama da shi a duk fadin kasar nan ba a iya Jihar Kwara ko shiyyar Arewa ta Tsakiya ya tsaya ba, yawancin ku a nan ‘yan kasa da shekara 30 ne kuma yawancin ku a nan ba su da aikin yi ko sana’a. Za mu tabbatar da cewa a cikin shirin namu na yi alkawarin cewa zan ware Dala biliyan 10 don ganin an samar da ayyukan yi ga matasa a kananan da matsakaitan sana’o’i don ba ku dama da kuma tabbatar da cewa an samar muku da ayyukan yi.

“Ba mu zo nan don mu muku karya ba, mu iyayenku ne, muna son ku zama kamar yadda muke, za mu ba ku dama, za mu kawo ku, za mu tabbatar kun cimma burinku, ko mene ne. Babban burin ku, shi ya sa muke nan, kar ku sake zabar APC, ku zabi duk ‘yan takarar PDP a 2023.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Mun kuma yi alkawarin dawo da tsaro a duk fadin kasar nan, lokacin da suka zo sai suka ce za su magance matsalar rashin tsaro nan a watanni shida, amma me muke gani? abubuwan da ke faruwa,” in ji Atiku.

Dan takarar shugaban kasar ya bukaci ’yan Kwara da su zabi dukkan ‘yan takarar PDP a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku, wanda ya ce a ranar Laraba ne jam’iyyar ta kaddamar da kwamitin mata na PDP, ya kara da cewa ita ce ta farko a tarihin babbar jam’iyyar adawa.

Ya yaba wa al’ummar Jihar Kwara bisa yawan fitowar jama’a tare da gode musu bisa goyon bayan da suka samu da kuma tarbar da tawagar yakin neman zabensa suka yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version