• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Minista Ya Nemi Jama’a Su Ƙara Haƙuri, Gwamnati Na Ƙoƙarin Rage Tsadar Rayuwa 

by Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya, musamman matasa masu shirin zanga-zanga, da su yi haƙuri.

 

A halin yanzu wasu ‘yan Nijeriya na ta yin shelar cewa, za su yi zanga-zangar lumana a ƙarshen wannan watan domin bayyana ɓacin ransu kan matsin tattalin arziki da ake fuskanta a kasar.

  • Tinubu Ya Aike Wa Majalisa Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Don Tantancewa
  • Abokan Kasuwancinmu Na Zuwa A Kai-A Kai Don Neman Man Da Muke Tacewa – Dangote 

A wata hira da ya yi da BBC Hausa a ranar Asabar, ministan ya ce, Gwamnatin Tarayya ta ɗauki wasu muhimman matakai domin magance matsalolin da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Ya ce: “Akwai mataki na farko da gwamnati ta ɗauka na a samu a raba kayan abinci ga al’ummar Nijeriya. An kai shinkafa jihohi duka ga baki ɗaya talatin da shida da kuma yankin Abuja.”

 

Ya ƙara da cewa, “Akwai wani shiri da ake yi na CNG, ma’ana wannan harka na iskar gas wanda duk motocin da za su yi aiki, za su yi aiki da wannan na’ura, wato ta iskar gas, misali idan kana kashe naira goma wajen sufuri yanzu kuɗin ka zai dawo ƙasa ma da naira huɗu. Ka ga an sake samun cigaba.

 

“In ka lura da abin da ake yi kamar na bututun gas na AKK wanda kwanakin baya an je Kaduna an sake duba shi, ya kai kusan wato kashi casa’in da biyar da gamawa. Abu ne da aka fara tun waccan gwamnatin da ta shuɗe.

 

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da kuma ya tsaya tsayin daka lallai a samu a gama wannan shiri saboda idan aka yi shi za a samu sauƙi sosai.

 

“Duk kamfanonin da aka rurrufe saboda matsalar wutar lantarki da ɗimbin al’umma da suka rasa ayyukan su saboda rufe kamfanunnuka idan Allah ya yarda za su dawo.”

 

Ministan ya yi nuni da cewa Shugaban Ƙasa ya ƙaddamar da Shirin Lamunin Ɗalibai don ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi su samu damar zuwa makaranta.

 

Ya ce: “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kuma ƙaddamar da harkar wato abin da ake ce ma Student Loan, wato bashi saboda a yi makaranta. Yana takaicin cewa bai kamata a ce wani yaro bai iya zuwa makaranta ba saboda iyayen sa ba su da kuɗin biya masa makaranta.

 

“Yanzu duk wani wanda ya iya cin jarabawa, duk wani yaro ɗan Nijeriya, cikakken ɗan Nijeriya da ya iya cin jarabawa, zai iya zuwa ya amfana a biya masa bashi mai sauƙi cikin rahusa ya biya kuɗin makaranta, ba ma kawai a biya kuɗin makaranta ba, ya samu kuɗin da kuma zai iya ɓatarwa har ya gama karatun sa.”

 

Dangane da wahalhalun da ‘yan Nijeriya ke fuskanta duk da alƙawurran da Shugaba Tinubu ya yi na kawo sauƙin rayuwa, Idris ya ce: “Lallai gwamnati ta yarda cewa akwai wannan matsatsi. Abin da ya bambanta gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatoci da yawa shi ne idan akwai matsala akan amsa a ce lallai akwai matsala a wuri kaza amma kuma ga abin da mu ke yi na a samo maslaha.

 

“A yanzu maganar da ake yi a harkar tsaro abin da muke ciki misali shekara ɗaya baya, ko shekara biyu baya, ai ka ga abin ba haka ba ne.

 

“Mu na fata a haɗa ƙarfi da ƙarfe, su mutanen ƙasa su ba gwamnati goyon baya domin a kawo ƙarshen wannan al’amari.

 

“Saboda haka a ƙara yin haƙuri, kiran da gwamnati ke yi kenan. A ƙara yi wa gwamnati haƙuri, idan Allah ya yarda a hankali a hankali za a kawo ƙarshen wannan al’amari.”

 

Ministan ya ce akwai tanadi da gwamnati ta yi wa manoma inda Babban Bankin Nijeriya (CBN), ta hanyar Ma’aikatar Aikin Gona, ya raba taki buhu miliyan dubu ɗari ɗaya da hamsin ga manoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsadar RayuwaZanga-zangar lumana
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Taya Kagame Murna Bisa Sake Zabarsa A Matsayin Shugaban Rwanda

Next Post

Wang Yi: PLO Ita Ce Kadai Halatacciyar Wakiliyar Al’ummar Falasdinu

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

49 minutes ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

3 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

6 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

7 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

7 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

8 hours ago
Next Post
Wang Yi: PLO Ita Ce Kadai Halatacciyar Wakiliyar Al’ummar Falasdinu

Wang Yi: PLO Ita Ce Kadai Halatacciyar Wakiliyar Al’ummar Falasdinu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.