• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zanga: Kebbi Ta Bukaci Matasa Da Su Guji Tashe-tashen Hankula

by Sulaiman and Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Zanga-zanga: Kebbi Ta Bukaci Matasa Da Su Guji Tashe-tashen Hankula
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani kakkausan kira na wanzar da zaman lafiya, Shugaban Ma’aikatan jihar Kebbi, Alhaji Sifiyanu Garba Bena, ya bukaci matasa da ma’aikata a Nijeriya da su guji shiga ayyukan ‘yan daba a yayin gudanar da zanga-zangar da ake shirin gudanar wa a fadin Nijeriya.

 

Da yake jawabi ga manema labarai a safiyar ranar Alhamis a ofishinsa da ke Birnin Kebbi, Shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Sifiyanu Garba Bena ya jaddada cewa, duk da cewa zanga-zangar lumana hakki ne da tsarin mulki ya tanada, amma bai kamata a yi barna ko tada fitina a tsakanin al’umma ba.

  • Zanga-zanga-zanga: Tinubu Ya Yi Taron Gaggawa Da Manyan Sarakunan Gargajiya A Abuja
  • Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha’anin Tsaro

“Mun amince da mutunta ‘yancin matasanmu na bayyana damuwarsu ta hanyar zanga-zangar lumana, amma muna yin Allah-wadai da duk wani nau’i na tashin hankali, lalata dukiyoyin jama’a ko ta gwamnati, da duk wani aiki da zai iya rikidewa zuwa rikici tsakanin al’umma.” In ji Bena

 

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

Wannan kiran  na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun tashe-tashen hankula bayan zanga-zangar baya-bayan nan da ta rikide zuwa tashe tashen hankula, lamarin da ya janyo hasarar dimbin ababen more rayuwa na gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu.

 

Don haka, ana kara nuna damuwa kan illar da ka iya haifar da tarzoma ga zaman lafiya da hadin kan al’umma a fadin Nijeriya.

 

Alhaji Sifiyanu Garba Bena ya bukaci masu ruwa da tsaki musamman wadanda suka shirya zanga-zangar da su ba da fifiko wajen fadin albarkacin bakinsu tare da kaucewa ayyukan da za su kawo cikas ga tsaro da zamantakewar al’umma a jahohin Nijeriya.

 

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shirya tsaf domin kare lafiyar jama’a tare da mutunta ‘yancin ‘yan kasa.

 

“Muna aiki kafada da kafada da jami’an tsaro domin ganin an samar da isassun matakan kare rayuka da dukiyoyi a yayin zanga-zangar,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaRashin TsaroTabarbarewar IlimiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Hatsi Da Sin Ta Samu Ya Zarce Kg Biliyan 650 Cikin Shekaru 9 A Jere

Next Post

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Related

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

2 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Labarai

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

5 hours ago
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

6 hours ago
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike
Manyan Labarai

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

9 hours ago
Next Post
Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.