• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

by Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Ci Gaba Da Ingiza Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

{"ARInfo":{"IsUseAR":false},"Version":"1.0.0","MakeupInfo":{"IsUseMakeup":false},"FaceliftInfo":{"IsChangeEyeLift":false,"IsChangeFacelift":false,"IsChangePostureLift":false,"IsChangeNose":false,"IsChangeFaceChin":false,"IsChangeMouth":false,"IsChangeThinFace":false},"BeautyInfo":{"SwitchMedicatedAcne":false,"IsAIBeauty":false,"IsBrightEyes":false,"IsSharpen":false,"IsOldBeauty":false,"IsReduceBlackEyes":false},"HandlerInfo":{"AppName":2},"FilterInfo":{"IsUseFilter":false}}

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A watannin 6 na farkon shekarar bana alkaluma sun tabbatar da cewa tattalin arzikin kasar Sin na ci gaba da farfadowa da bunkasa bisa daidaito. Kaza lika, a ranar 16 ga watan nan ma asusun IMF ya fitar da sabon hasashen bunkasar tattalin arzikin duniya, wanda ya nuna yiwuwar bunkasar tattalin arzikin kasar Sin da kaso 5 bisa dari a bana, wanda hakan ya nuna karuwar kaso 0.4 bisa dari kan hasashen da asusun ya fitar a watan Afrilun da ya gabata.

 

Masharhanta na cewa wannan hasashe na bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, zai samar da karsashi na dogon lokaci ga farfadowa, da bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya. IMF dai ya amince cewa bunkasar tattalin arzikin kasashen Asiya masu samun saurin ci gaba ciki har da Sin, shi ne jigon bunkasar tattalin arzikin duniya, musamman a gabar da tattalin arzikin Sin ke kara habaka ta fuskar yawa da kuma inganci.

  • Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Arewa Da Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Sun Buƙaci Matasa Su Kaucewa Shiga Zanga-zanga
  • Wasu Ɓata-gari Na Iya Amfani Da Zanga-zanga Domin Tada Zaune Tsaye – Minista

Alkaluma sun nuna cewa a wa’adin watanni 6 na farkon shekarar nan ta 2024, ma’aunin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin na GDP ya karu da kaso 5 bisa dari, inda darajarsa ta kai kudin kasar yuan tiriliyan 61.7, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 8.49. Tsakanin wannan wa’adi, adadin sayayyar kayayyakin bukatun al’umma a kasar ta Sin, da hidimomi masu nasaba da hakan duk sun karu, yayin da jarin da ake kara zubawa a fannin samar da ababen more rayuwa ya daga da kaso 5.4 bisa dari kan na makamancin lokaci na bara.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Karin sassan dake bunkasa sun hada da na sarrafa hajoji a masana’antu, da cinikayyar waje, wadda a wannan wa’adi darajarta ta kai kudin Sin yuan tiriliyan 21.2. Bisa dukkanin shaidu, tun daga mahanga ta kusa har zuwa tsawon lokaci mai zuwa, sassan tattalin arzikin kasar Sin za su ci gaba da bunkasa, yayin da kasar ke kara samun bunkasuwa mai inganci.

 

Idan an yi duba na tsanaki, abu ne mai sauki a gano dalilan da suka haifar da wannan nasara da kasar Sin ke samu. Ga misali bunkasar sarrafa hajojin masana’antu masu kunshe da fasahohin zamani, da sarrafa hajoji ba tare da gurbata muhalli ba sun taka rawar gani wajen ingiza tattalin arzikin kasar Sin.

 

Kaza lika fannin bunkasar sabbin fannonin samar da hajoji irin su kayayyaki masu amfani da kirkirarriyar basira, da fasahar sarrafa manyan bayanai, da hidimomin sayyaya ta yanar gizo, dukkaninsu sun baiwa kasar damar cin karin gajiya.

 

Har ila yau, kwazon kasar Sin na zurfafa gyare-gyare a dukkanin fannoni ya samar da sabon karfi na ingiza ci gaba mai inganci, da nasarar matakan zamanantarwa irin ta Sin. Masana da masharhanta sun yi imanin cewa tattalin arzikin kasar Sin zai sauya daga tsohon matakinsa zuwa sabon salo mai inganci, karkashin manufofin zurfafa gyare-gyare da kara bude kofofin kasar ga kasashen waje.

 

Yayin da ake fatan cimma nasarar hakan, kasar Sin ta wanzar da alakar cinikayya da sama da kasashen duniya da yankuna 140, wanda hakan ya sanya jimillar hada hadar hajojin kasuwancinta da kasashen waje ya kai matsayin farko a duniya cikin shekaru 7 a jere.

 

Bugu da kari, shawarar “ziri daya da hanya daya” ko BRI da kasar Sin ta gabatar ita ma na taka rawar ganin wajen dinke kasar da sauran sassan duniya ta fuskar cimma moriyar juna, inda kawo yanzu sama da kasashen duniya 150, da hukumomin kasa da kasa 30 suka shiga wannan shawara mai riba.

 

Masharhanta na ganin wannan ci gaba da Sin ke samu, dama ce ta musamman ga daukacin duniya ta morewa fasahohin Sin, da cimma moriyar juna, ta yadda dukkanin sassan duniya za su hada gwiwa domin a gudu tare a tsira tare. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-zanga: Kebbi Ta Bukaci Matasa Da Su Guji Tashe-tashen Hankula

Next Post

CMG Ta Fitar Da Ma’aunin Watsa Labarai Kai Tsaye Na Wasannin Olympics Na Paris Da Kuma Kafa Studiyonta A Gaban Eiffel

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

9 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

10 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

11 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

12 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

13 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

15 hours ago
Next Post
CMG Ta Fitar Da Ma’aunin Watsa Labarai Kai Tsaye Na Wasannin Olympics Na Paris Da Kuma Kafa Studiyonta A Gaban Eiffel

CMG Ta Fitar Da Ma’aunin Watsa Labarai Kai Tsaye Na Wasannin Olympics Na Paris Da Kuma Kafa Studiyonta A Gaban Eiffel

LABARAI MASU NASABA

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.