• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zarge-zargen Shugaban Sojin Nijar Kan Nijeriya Ba Su Da Tushe – Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Sojin ƙasar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani, ya yi a cikin wani faifan bidiyo da ke yawo, inda ya zargi Nijeriya da haɗa kai da Faransa domin tayar da zaune tsaye a ƙasar sa.  

 

A cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Alhamis, gwamnati ta bayyana zargin a matsayin “mara tushe kuma wanda aka ƙirƙira kawai.”

  • Ƙasa Da Sa’o’i 30 Da Rasuwar Mahaifiyarsa, Gwamnan Jigawa Ya Sake Rasa Ɗansa A Hatsarin Mota 
  • Sin Ta Gabatar Da Rukuni 2 Na Kayayyakin Agajin Gaggawa Ga Al’ummun Gaza Ta Mashigin Kasar Masar

“Nijeriya ba ta taɓa shiga wata yarjejeniya ta ɓoye ko ta fili da Faransa—ko wata ƙasa—ba domin ɗaukar nauyin hare-haren ta’addanci ko tayar da zaune tsaye a Jamhuriyar Nijar,” inji Idris.

 

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a matsayin sa na Shugaban Ƙungiyar Haɗa Kan Yankin Afrika ta Yamma (ECOWAS), ya nuna bajinta ta shugabanci, inda ya ci gaba da buɗe ƙofa ta diflomasiyya da Nijar duk da rikicin siyasa da ake fuskanta a ƙasar.

 

Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai da kyakkyawar alaƙa da Nijar.

 

Haka kuma ya musanta zargin cewa Nijeriya tana yunƙurin lalata bututun mai da harkar noman Nijar, ya kira wannan zargin “mara tushe kuma mai cutarwa.”

 

Ya ce Nijeriya ta daɗe tana taimaka wa bunƙasar tattalin arzikin Nijar ta hanyar manyan ayyuka na haɗin gwiwa kamar bututun iskar gas da ya ratsa Sahara da kuma layin dogo na Kano zuwa Maraɗi.

 

Nijeriya ta kuma ƙaryata iƙirarin cewa wai an kafa wata hedikwatar ta’addanci ta Lakurawa a Jihar Sakkwato tare da haɗin baki tsakanin Nijeriya da Faransa.

 

Idris ya musanta wannan batu, yana mai bayyana jagorancin da Nijeriya ke yi wajen yaƙar ta’addanci a yankin, ciki har da shirin nan na ‘Operation Forest Sanity III’ wanda aka ƙaddamar kwanan nan.

 

“Ta yaya za a zargi gwamnatin da ke ƙoƙarin yaƙar barazanar Lakurawa da ɓoye ƙungiyar a cikin ƙasar ta?” inji Idris, yana mai bayyana zargin a matsayin mara gamsasshiyar hujja da kuma wani ƙoƙari na karkatar da hankali daga matsalolin cikin gida da Nijar ke fuskanta.

 

Ministan ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da waɗannan ƙarairayi, yana ƙalubalantar Tchiani da ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi don tabbatar da zarge-zargen sa.

 

Ya bayyana duk wani yunƙuri na yi wa Nijeriya barazana kan matsayar ECOWAS na adawa da karɓar mulki ba bisa doka ba da aka yi a Nijar a matsayin “mai cike da yaudara kuma wanda ba zai cimma nasara ba.”

 

“Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a yankin tare da jagorantar ƙoƙarin magance matsalolin ta’addanci da sauran ƙalubale na ƙetare,” inji Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Mika Jaje Game Da Hadarin Jirgin Saman Azerbaijan

Next Post

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

3 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

3 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

4 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

5 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

6 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.