• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zarge-zargen Shugaban Sojin Nijar Kan Nijeriya Ba Su Da Tushe – Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Sojin ƙasar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani, ya yi a cikin wani faifan bidiyo da ke yawo, inda ya zargi Nijeriya da haɗa kai da Faransa domin tayar da zaune tsaye a ƙasar sa.  

 

A cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Alhamis, gwamnati ta bayyana zargin a matsayin “mara tushe kuma wanda aka ƙirƙira kawai.”

  • Ƙasa Da Sa’o’i 30 Da Rasuwar Mahaifiyarsa, Gwamnan Jigawa Ya Sake Rasa Ɗansa A Hatsarin Mota 
  • Sin Ta Gabatar Da Rukuni 2 Na Kayayyakin Agajin Gaggawa Ga Al’ummun Gaza Ta Mashigin Kasar Masar

“Nijeriya ba ta taɓa shiga wata yarjejeniya ta ɓoye ko ta fili da Faransa—ko wata ƙasa—ba domin ɗaukar nauyin hare-haren ta’addanci ko tayar da zaune tsaye a Jamhuriyar Nijar,” inji Idris.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a matsayin sa na Shugaban Ƙungiyar Haɗa Kan Yankin Afrika ta Yamma (ECOWAS), ya nuna bajinta ta shugabanci, inda ya ci gaba da buɗe ƙofa ta diflomasiyya da Nijar duk da rikicin siyasa da ake fuskanta a ƙasar.

 

Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai da kyakkyawar alaƙa da Nijar.

 

Haka kuma ya musanta zargin cewa Nijeriya tana yunƙurin lalata bututun mai da harkar noman Nijar, ya kira wannan zargin “mara tushe kuma mai cutarwa.”

 

Ya ce Nijeriya ta daɗe tana taimaka wa bunƙasar tattalin arzikin Nijar ta hanyar manyan ayyuka na haɗin gwiwa kamar bututun iskar gas da ya ratsa Sahara da kuma layin dogo na Kano zuwa Maraɗi.

 

Nijeriya ta kuma ƙaryata iƙirarin cewa wai an kafa wata hedikwatar ta’addanci ta Lakurawa a Jihar Sakkwato tare da haɗin baki tsakanin Nijeriya da Faransa.

 

Idris ya musanta wannan batu, yana mai bayyana jagorancin da Nijeriya ke yi wajen yaƙar ta’addanci a yankin, ciki har da shirin nan na ‘Operation Forest Sanity III’ wanda aka ƙaddamar kwanan nan.

 

“Ta yaya za a zargi gwamnatin da ke ƙoƙarin yaƙar barazanar Lakurawa da ɓoye ƙungiyar a cikin ƙasar ta?” inji Idris, yana mai bayyana zargin a matsayin mara gamsasshiyar hujja da kuma wani ƙoƙari na karkatar da hankali daga matsalolin cikin gida da Nijar ke fuskanta.

 

Ministan ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da waɗannan ƙarairayi, yana ƙalubalantar Tchiani da ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi don tabbatar da zarge-zargen sa.

 

Ya bayyana duk wani yunƙuri na yi wa Nijeriya barazana kan matsayar ECOWAS na adawa da karɓar mulki ba bisa doka ba da aka yi a Nijar a matsayin “mai cike da yaudara kuma wanda ba zai cimma nasara ba.”

 

“Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a yankin tare da jagorantar ƙoƙarin magance matsalolin ta’addanci da sauran ƙalubale na ƙetare,” inji Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Mika Jaje Game Da Hadarin Jirgin Saman Azerbaijan

Next Post

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Related

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

2 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

4 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

5 hours ago
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi
Labarai

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

6 hours ago
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Manyan Labarai

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

7 hours ago
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
Manyan Labarai

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.