• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zarge-zargen Shugaban Sojin Nijar Kan Nijeriya Ba Su Da Tushe – Gwamnatin Tarayya

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Sojin ƙasar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani, ya yi a cikin wani faifan bidiyo da ke yawo, inda ya zargi Nijeriya da haɗa kai da Faransa domin tayar da zaune tsaye a ƙasar sa.  

 

A cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya fitar a ranar Alhamis, gwamnati ta bayyana zargin a matsayin “mara tushe kuma wanda aka ƙirƙira kawai.”

  • Ƙasa Da Sa’o’i 30 Da Rasuwar Mahaifiyarsa, Gwamnan Jigawa Ya Sake Rasa Ɗansa A Hatsarin Mota 
  • Sin Ta Gabatar Da Rukuni 2 Na Kayayyakin Agajin Gaggawa Ga Al’ummun Gaza Ta Mashigin Kasar Masar

“Nijeriya ba ta taɓa shiga wata yarjejeniya ta ɓoye ko ta fili da Faransa—ko wata ƙasa—ba domin ɗaukar nauyin hare-haren ta’addanci ko tayar da zaune tsaye a Jamhuriyar Nijar,” inji Idris.

 

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Ministan ya jaddada cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a matsayin sa na Shugaban Ƙungiyar Haɗa Kan Yankin Afrika ta Yamma (ECOWAS), ya nuna bajinta ta shugabanci, inda ya ci gaba da buɗe ƙofa ta diflomasiyya da Nijar duk da rikicin siyasa da ake fuskanta a ƙasar.

 

Idris ya tabbatar da cewa Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai da kyakkyawar alaƙa da Nijar.

 

Haka kuma ya musanta zargin cewa Nijeriya tana yunƙurin lalata bututun mai da harkar noman Nijar, ya kira wannan zargin “mara tushe kuma mai cutarwa.”

 

Ya ce Nijeriya ta daɗe tana taimaka wa bunƙasar tattalin arzikin Nijar ta hanyar manyan ayyuka na haɗin gwiwa kamar bututun iskar gas da ya ratsa Sahara da kuma layin dogo na Kano zuwa Maraɗi.

 

Nijeriya ta kuma ƙaryata iƙirarin cewa wai an kafa wata hedikwatar ta’addanci ta Lakurawa a Jihar Sakkwato tare da haɗin baki tsakanin Nijeriya da Faransa.

 

Idris ya musanta wannan batu, yana mai bayyana jagorancin da Nijeriya ke yi wajen yaƙar ta’addanci a yankin, ciki har da shirin nan na ‘Operation Forest Sanity III’ wanda aka ƙaddamar kwanan nan.

 

“Ta yaya za a zargi gwamnatin da ke ƙoƙarin yaƙar barazanar Lakurawa da ɓoye ƙungiyar a cikin ƙasar ta?” inji Idris, yana mai bayyana zargin a matsayin mara gamsasshiyar hujja da kuma wani ƙoƙari na karkatar da hankali daga matsalolin cikin gida da Nijar ke fuskanta.

 

Ministan ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da waɗannan ƙarairayi, yana ƙalubalantar Tchiani da ya gabatar da hujjoji masu ƙarfi don tabbatar da zarge-zargen sa.

 

Ya bayyana duk wani yunƙuri na yi wa Nijeriya barazana kan matsayar ECOWAS na adawa da karɓar mulki ba bisa doka ba da aka yi a Nijar a matsayin “mai cike da yaudara kuma wanda ba zai cimma nasara ba.”

 

“Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a yankin tare da jagorantar ƙoƙarin magance matsalolin ta’addanci da sauran ƙalubale na ƙetare,” inji Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Mika Jaje Game Da Hadarin Jirgin Saman Azerbaijan

Next Post

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

18 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

1 day ago
Next Post
Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

Sin Ta Bayyana Sakamakon Kidayar Harkokin Tattalin Arziki Karo Na 5

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.