• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta yi watsi da bukatar da aka shigar a gabanta ta neman bayar da belin Tukur Mohammed Manu da ake zargi da daukar nauyin ta’addanci.

Alkalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ne ya dauki wannan matakin a zaman kotun aka yi a yau Alhamis, inda ya ce, takardar neman belin Manu babu wasu gamsassun hujjoji a cikinta da za ta sa, kotun ta bayar da belinsa.

  • Za A Yi Taron Koli Tsakannin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya A Watan Mayu A Xi’an
  • Zaben Adamawa: A Hukunta Kwamishinan Zaben Adamawa -Fintiri

Ekwo ya ce, Mamau ya gaza kare kansa, inda ya ce, mai yiwuwa wanda ake tuhumar ya kara aikata wasu laifukan.

Ya ci gaba da cewa, a bisa ka’idar doka idan har wanda ake tukuma ya gaza kare kansa zargin da ake yi masa, zai iya zamo wa gaskiya domin abin da aka gabatar wa kotun ana bukatar karin hujja daga wajen wanda kotun ke tuhuma.

Sai dai, alkalin ya ce wanda kotun ke tuhuma ya yi ikirarin cewa, wajen da hukumar jami’an tsaro ta farin kaya ta jiha ta ajiye shi (SSS), ba zai iya samun kalubalen rashin lafiyar da yake fama da ita ba, inda ya ce, kotun za ta yi duba kan hakan, kafin ta dauki mataki na gaba.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

A cewar Ekwo, kotun za ta auna hujjojin don ganin ko wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar za su bashi damar zuwa a duba tafiyarsa.

Ya ce, hukumar ta SSS, na da kayan kiwon lafiya da za ta iya duba tafiyar wanda ake tuhumar yadda ya kamata, sai dai, ya bayyana cewa, kotun ba za ta yi jayayya da takarar neman belin zuwa neman lafiyar wanda ake tuhumar ba.

Alkalin ya kara da cewa, idan wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar ba su da kayan aikin da za su duba tafiyar wanda ake tuhumar ba, amma za su iya tabbatar da samar masa da asibtin da za a duba tafiyarsa dai-dai da irin ciwon da yake fama da shi, kotun ba za ta iya bayar da belinsa ba.

Ya ci gaba da cewa, a yanzu idan wanda kotun ke tuhuma yaki amincewa da inda wadanda ke ajiya da shi suka samar masa wurin da za a duba tafiyarsa amma asibitin ya kasance matsayin da shi wanda ake tuhumar yake so ba, saboda haka bai da wata hujjar a bayar da belinsa.

Ya ce, wanda ake tuhuma da ke ake tsare da shi a jiha ko a hannun hukumar tsaro kamar mai korafi ko wanda ake tuhuma a hannun DSS, dole ne su fahimci kudin da za a kashe na duba tafiyarsa ya kasance su biya daga aljihun jihar da kuma duba bukatunsa.

Ya ce, hujjar da ke gaban kotun ta nuna cewa, bayan wanda kotun ke tuhumar yaki amincewa da a duba tafiyarsa a asibitin DSS, hukumar ta kai shi kwararren asibitin Arewa da kuma cibiyar kiwon lafiya da ke a Jabi.

Ya ce, a asibitin Arewa an yi masa gwaje-gwajen lafiyarsa yadda ta kamata.

Alkalin ya kara da cewa, DSS ta tabbar da cewa, asibitin ya duba tafiyarsa yadda ta kamata kuma a shirye ta ke, ta biya kudin da aka duba tafiyar Mamu.

Ya ce, DSS ta tabbatar da samar da dama ga Mamu wajen kula da lafiyarsa ta yau da kullum a yayin da yake ci gaba fuskantar shari’a, inda ya ce, bisa wadanan hujojin, maganar bayar da belinsa ba ta taso ba kamar yadda sashen doka na 1 da na 2 na dokar ACJA ta 2015 ta tanada.

Alkalin ya ce saboda haka kotun ta yi watsi da takardar bukatar bayar da belin nasa.

Gwamnatin tarayya ce ta gurfanar da Mamu a ranar 21 ga watan Maris kan tuhuma 10 ciki har da ta daukar nauyin ta’addanci da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeliKotuTukur Mamu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Taron Koli Tsakannin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya A Watan Mayu A Xi’an

Next Post

An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

10 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

21 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.