ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu

by Abubakar Abba
3 years ago
Mamu

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta yi watsi da bukatar da aka shigar a gabanta ta neman bayar da belin Tukur Mohammed Manu da ake zargi da daukar nauyin ta’addanci.

Alkalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ne ya dauki wannan matakin a zaman kotun aka yi a yau Alhamis, inda ya ce, takardar neman belin Manu babu wasu gamsassun hujjoji a cikinta da za ta sa, kotun ta bayar da belinsa.

  • Za A Yi Taron Koli Tsakannin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya A Watan Mayu A Xi’an
  • Zaben Adamawa: A Hukunta Kwamishinan Zaben Adamawa -Fintiri

Ekwo ya ce, Mamau ya gaza kare kansa, inda ya ce, mai yiwuwa wanda ake tuhumar ya kara aikata wasu laifukan.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa, a bisa ka’idar doka idan har wanda ake tukuma ya gaza kare kansa zargin da ake yi masa, zai iya zamo wa gaskiya domin abin da aka gabatar wa kotun ana bukatar karin hujja daga wajen wanda kotun ke tuhuma.

Sai dai, alkalin ya ce wanda kotun ke tuhuma ya yi ikirarin cewa, wajen da hukumar jami’an tsaro ta farin kaya ta jiha ta ajiye shi (SSS), ba zai iya samun kalubalen rashin lafiyar da yake fama da ita ba, inda ya ce, kotun za ta yi duba kan hakan, kafin ta dauki mataki na gaba.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

A cewar Ekwo, kotun za ta auna hujjojin don ganin ko wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar za su bashi damar zuwa a duba tafiyarsa.

Ya ce, hukumar ta SSS, na da kayan kiwon lafiya da za ta iya duba tafiyar wanda ake tuhumar yadda ya kamata, sai dai, ya bayyana cewa, kotun ba za ta yi jayayya da takarar neman belin zuwa neman lafiyar wanda ake tuhumar ba.

Alkalin ya kara da cewa, idan wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar ba su da kayan aikin da za su duba tafiyar wanda ake tuhumar ba, amma za su iya tabbatar da samar masa da asibtin da za a duba tafiyarsa dai-dai da irin ciwon da yake fama da shi, kotun ba za ta iya bayar da belinsa ba.

Ya ci gaba da cewa, a yanzu idan wanda kotun ke tuhuma yaki amincewa da inda wadanda ke ajiya da shi suka samar masa wurin da za a duba tafiyarsa amma asibitin ya kasance matsayin da shi wanda ake tuhumar yake so ba, saboda haka bai da wata hujjar a bayar da belinsa.

Ya ce, wanda ake tuhuma da ke ake tsare da shi a jiha ko a hannun hukumar tsaro kamar mai korafi ko wanda ake tuhuma a hannun DSS, dole ne su fahimci kudin da za a kashe na duba tafiyarsa ya kasance su biya daga aljihun jihar da kuma duba bukatunsa.

Ya ce, hujjar da ke gaban kotun ta nuna cewa, bayan wanda kotun ke tuhumar yaki amincewa da a duba tafiyarsa a asibitin DSS, hukumar ta kai shi kwararren asibitin Arewa da kuma cibiyar kiwon lafiya da ke a Jabi.

Ya ce, a asibitin Arewa an yi masa gwaje-gwajen lafiyarsa yadda ta kamata.

Alkalin ya kara da cewa, DSS ta tabbar da cewa, asibitin ya duba tafiyarsa yadda ta kamata kuma a shirye ta ke, ta biya kudin da aka duba tafiyar Mamu.

Ya ce, DSS ta tabbatar da samar da dama ga Mamu wajen kula da lafiyarsa ta yau da kullum a yayin da yake ci gaba fuskantar shari’a, inda ya ce, bisa wadanan hujojin, maganar bayar da belinsa ba ta taso ba kamar yadda sashen doka na 1 da na 2 na dokar ACJA ta 2015 ta tanada.

Alkalin ya ce saboda haka kotun ta yi watsi da takardar bukatar bayar da belin nasa.

Gwamnatin tarayya ce ta gurfanar da Mamu a ranar 21 ga watan Maris kan tuhuma 10 ciki har da ta daukar nauyin ta’addanci da sauransu.

Mamu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.