ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Daukar Nauyin Ta’addanci: Kotu Ta Hana Belin Tukur Mamu

by Abubakar Abba
3 years ago
Mamu

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta yi watsi da bukatar da aka shigar a gabanta ta neman bayar da belin Tukur Mohammed Manu da ake zargi da daukar nauyin ta’addanci.

Alkalin kotun mai shari’a Inyang Ekwo ne ya dauki wannan matakin a zaman kotun aka yi a yau Alhamis, inda ya ce, takardar neman belin Manu babu wasu gamsassun hujjoji a cikinta da za ta sa, kotun ta bayar da belinsa.

  • Za A Yi Taron Koli Tsakannin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya A Watan Mayu A Xi’an
  • Zaben Adamawa: A Hukunta Kwamishinan Zaben Adamawa -Fintiri

Ekwo ya ce, Mamau ya gaza kare kansa, inda ya ce, mai yiwuwa wanda ake tuhumar ya kara aikata wasu laifukan.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa, a bisa ka’idar doka idan har wanda ake tukuma ya gaza kare kansa zargin da ake yi masa, zai iya zamo wa gaskiya domin abin da aka gabatar wa kotun ana bukatar karin hujja daga wajen wanda kotun ke tuhuma.

Sai dai, alkalin ya ce wanda kotun ke tuhuma ya yi ikirarin cewa, wajen da hukumar jami’an tsaro ta farin kaya ta jiha ta ajiye shi (SSS), ba zai iya samun kalubalen rashin lafiyar da yake fama da ita ba, inda ya ce, kotun za ta yi duba kan hakan, kafin ta dauki mataki na gaba.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A cewar Ekwo, kotun za ta auna hujjojin don ganin ko wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar za su bashi damar zuwa a duba tafiyarsa.

Ya ce, hukumar ta SSS, na da kayan kiwon lafiya da za ta iya duba tafiyar wanda ake tuhumar yadda ya kamata, sai dai, ya bayyana cewa, kotun ba za ta yi jayayya da takarar neman belin zuwa neman lafiyar wanda ake tuhumar ba.

Alkalin ya kara da cewa, idan wadanda ke tsare da wanda ake tuhumar ba su da kayan aikin da za su duba tafiyar wanda ake tuhumar ba, amma za su iya tabbatar da samar masa da asibtin da za a duba tafiyarsa dai-dai da irin ciwon da yake fama da shi, kotun ba za ta iya bayar da belinsa ba.

Ya ci gaba da cewa, a yanzu idan wanda kotun ke tuhuma yaki amincewa da inda wadanda ke ajiya da shi suka samar masa wurin da za a duba tafiyarsa amma asibitin ya kasance matsayin da shi wanda ake tuhumar yake so ba, saboda haka bai da wata hujjar a bayar da belinsa.

Ya ce, wanda ake tuhuma da ke ake tsare da shi a jiha ko a hannun hukumar tsaro kamar mai korafi ko wanda ake tuhuma a hannun DSS, dole ne su fahimci kudin da za a kashe na duba tafiyarsa ya kasance su biya daga aljihun jihar da kuma duba bukatunsa.

Ya ce, hujjar da ke gaban kotun ta nuna cewa, bayan wanda kotun ke tuhumar yaki amincewa da a duba tafiyarsa a asibitin DSS, hukumar ta kai shi kwararren asibitin Arewa da kuma cibiyar kiwon lafiya da ke a Jabi.

Ya ce, a asibitin Arewa an yi masa gwaje-gwajen lafiyarsa yadda ta kamata.

Alkalin ya kara da cewa, DSS ta tabbar da cewa, asibitin ya duba tafiyarsa yadda ta kamata kuma a shirye ta ke, ta biya kudin da aka duba tafiyar Mamu.

Ya ce, DSS ta tabbatar da samar da dama ga Mamu wajen kula da lafiyarsa ta yau da kullum a yayin da yake ci gaba fuskantar shari’a, inda ya ce, bisa wadanan hujojin, maganar bayar da belinsa ba ta taso ba kamar yadda sashen doka na 1 da na 2 na dokar ACJA ta 2015 ta tanada.

Alkalin ya ce saboda haka kotun ta yi watsi da takardar bukatar bayar da belin nasa.

Gwamnatin tarayya ce ta gurfanar da Mamu a ranar 21 ga watan Maris kan tuhuma 10 ciki har da ta daukar nauyin ta’addanci da sauransu.

Mamu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.