• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Kabarin Annabi SAW (3)

by Sulaiman and Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Ci gaba daga makon jiya…

Imamul Fakihani, ya ce “wurin da aka binne Manzon Allah (SAW) ya fi sama ya fi kasa”. Haka nan, Alkadiy Iyad ya ce “Babu wani wurin da ya kai a hada shi da wurin da aka binne jikin Manzon Allah (SAW) saboda abu biyu: na farko, cewar da aka yi ko wane mutum ana binne shi a kasar da aka yi shi da ita, to nan wurin da aka binne Manzon Allah (SAW) kasar jikinsa ne, to wane abu ne za a iya hada shi da jikinsa (SAW)? Na biyu, bisa irin Mala’ikun da suke sauka a nan wurin, da irin albarkar da take sauka, da salatin da ake aikawa da sauran alheran da ke sauka a wurin, babu wani wurin da ya kai shi.”
Abu Ya’ala ya ruwaito Hadisi daga Sayyidina Abubakar (RA) ya ce, ya ji Manzon Allah (SAW) ya ce “Allah ba ya karbar Annabinsa sai a wurin da Annabin ya fi so.” Sayyidina Abubakar ya fadi Hadisin ne lokacin da Annabi (SAW) ya yi wafati sa’ilin da aka samu sabani kan wuri mafi dacewa a binne shi (SAW). Saboda haka suka ce babu shakka wurin da Annabi (SAW) ya fi so, nan ne Allah ya fi so. Domin son sa, yana biye ne da son Allah (SWT).
Imamun Nabahani ya ce, “Ziyarar kabarin Annabi (SAW) ita ce mafi girman kusanci zuwa ga Allah, ita ce mafi kaunar da’a ga Allah, ita ce hanyar da mutum zai bi ya samu kololuwar daraja. Duk wanda ya butulce ya ce ba haka ba, ya tube igiyar Musulunci daga wuyarsa. Kuma ya saba wa Allah, ya saba wa Annabi (SAW), ya saba wa tarin jama’ar malaman Musulunci na Allah.”
Alkadiy Iyad ya ce “Ziyarar Annabi (SAW) Sunnah ce daga sunnonin da Musulmi suka gaje ta kuma wacce aka hadu a kanta, falala ce abar kwadaitarwa.”
Darakudni ya ruwaito Hadisi daga Abdullahi bin Umar (RA) cewa, Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda ya ziyarci kabarina cetona ya wajaba a kansa.” Har ila yau, Darakudnin ya ruwaito daga Hadisin Abdullahi bin Umar (RA) cewa Manzon Allah (SAW) ya ce, “Duk wanda ya ziyarce ni bayan rasuwata kamar ya ziyarce ni ne ina cikin rayuwata”.
Zainuddin ibnil Husainil Maragiyu ya ce “Ya wajaba ga Musulmi ya kudurta cewa ziyarar Manzon Allah (SAW) kusanci ce; ibada ce saboda wadancan Hadisan guda biyu. Da kuma fadin Allah a cikin Alkur’ani cewa “da al’ummarka za su zalunci kansu sai su zo ma su nemi gafarar Allah a wajenka, kai kuma ka nema masu gafara, za su samu Allah mai karbar tuba da jinkai ne”.
Malamin sai ya kara da cewa “Manzon Allah (SAW) ya nema mana gafara, abin da ya rage sai mu je wurinsa, idan muka je sai mu nemi gafarar a gabansa. Shikenan abubuwa guda uku sun cika – mun je wurinsa, mun nemi gafara, ya nema mana gafara.”
Don haka, Alhajin da ya je ziyara kafin Arfa ya riga ya samu gafara tun kafin ranar Arfa sai ya zama garabasa biyu. Wanda kuma ya je bayan Arfa, abin da ya rage na daga zunubinsa da ya yi kafin zuwa ziyarar sai ya nemi gafarar a gaban Manzon Allah (SAW).
Ana so mai ziyara ya lizimci ladabi da kankar da kai, ya sunkuyar da ganinsa a yayin da yake ziyarar Annabi (SAW). Ya ji a ransa cewa ya zo wurin Annabi (SAW) kuma ga shi nan kamar yana ganinsa. Saboda babu banbanci tsakanin ziyararsa yana da rai da kuma bayan wafatinsa. Sannan mai ziyara ya rika tuna irin yadda su Sayyidina Abubakar (RA) suke ladabi a gabansa da magana a hankali. Kar mai ziyara ya yi kuru-kuru da ido, babu ladabi, babu natsuwa a tare da shi. Kar mutum ya kuskura ya bi maganganu wadanda suke raina janibinsa (SAW). Lamarin Annabi (SAW) ba na wasa ba ne, a kula da kyau.
Kuma ya kamata gwamnati ta kula da kyau, a rika samun jagororin mahajjata masu tsoron Allah da soyayyar Manzon Allah (SAW) don fadakar da Alhazai kan abin da ya fi zama daidai a Musulunci da Imani. Amma ba sharrori da munanan fahimta wanda da zarar mutum ya ji, ya san kiyayyar Manzon Allah (SAW) ce kawai ake koyar da mahajjata ba.
Hatta ita kanta Saudiyya yanzu abin ya dame ta, nema take ta gyara.
Akwai wasu da suke neman hana zuwa Madina ma kwata-kwata. Ko kuma su takura wa Alhazai a kan kar su yi kwana takwas din nan duk da cewa akwai Hadisi ingantacce kan haka.
Hadisin ba wai ya zo da adadin kwana takwas ne ba, amma yawan sallolin da Hadisin ya fada na adadin kwana takwas ne kamar yadda za mu kawo yanzu.
An karbo daga Anas bin Malik (RA), Annabi (SAW) ya ce “Duk wanda ya yi sallah a Masallacina guda arba’in ba tare da wata sallah ta tsere ma sa ba, za a rubuta ma sa takardar shaidar cewa ya kubuta daga wuta da duk wata azaba. Kuma zai kubuta daga munafunci.” Ahamdu bin Hambali ya ruwaito, shi ma Dabarani ya ruwaito da ingantaccen sanadi.
Idan aka buga lissafin sallolin farilla guda biyar da muke da su a rana, jimillar sallah 40 za ta zama ta kwana takwas.
Ya kamata a rika barin Alhazai suna samun wannan falalar. Abu ne da ya inganta a cikin Sunnar Annabi (SAW).
Kai ma mai ziyara ka san cewa ba hutu da shantakewa kawai za ka yi a Madina ba, ka yi kokari ikamar kowace sallah kar ta kubuce ma a Masallacin Annabi (SAW) idan ba akwai lalura mai karfin gaske ba.
Za mu dakata a nan sai Allah ya kai mu mako mai zuwa insha Allahu. Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadiy wa ala alihi hakka kadirihi wa mikdarihil aziym.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wajibi Ne Amurka Ta Cika Alkawarinta

Next Post

Barka Da Sabuwar Shekarar Hijira: Adamu Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Mallaki Katin Zaɓe

Related

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

6 days ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

2 weeks ago
Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

4 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

2 months ago
Next Post
Barka Da Sabuwar Shekarar Hijira: Adamu Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Mallaki Katin Zaɓe

Barka Da Sabuwar Shekarar Hijira: Adamu Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Mallaki Katin Zaɓe

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.