Shugaban kasar Aljeriya Abdelmadjid Tebboune ya isa filin jirgin sama na kasa da kasa na birnin Beijing domin ziyarar aiki ta kwanaki biyar a kasar Sin daga yau Litinin. Wannan dai ita ce ziyarar farko da shugaban na Aljeriya ya kai kasar Sin tun bayan hawansa mulki.Â
Da yake tsokaci don gane da ziyarar, shugaban kungiyar raya abota tsakanin Sin da Aljeriya, Isma’il Dabash, ya ce wannan ne karo na farko da shugaban na Aljeriya ya ziyarci kasar Sin tun bayan hawa karagar mulkin kasar, kuma ya yi imanin cewa, ziyarar za ta kara kyautata dangantakar abota dake tsakanin kasashen biyu.
A cewar Isma’il Dabash, kasar Sin ta taimakawa Aljeriya a shekarun 1950, lokacin da kasar ke fafutukar neman ‘yanci. Yana mai cewa, Sin ce kasa ta farko da ba ta Larabawa ba, da ta amince da kasar Aljeriya. Haka kuma Aljeriya a nata bangare, ta taimakawa Sin matuka, wajen dawo da halaltacciyar kujerarta a MDD. Ya ce shaidu sun nuna cewa Aljeriya da Sin sun kasance masu taimakon juna kuma aminai dake hadin gwiwa.
Bugu da kari, Isma’il Dabash ya ce Aljeriya ta shiga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya a shekarar 2018, kuma kasashen biyu sun rattaba hannu kan shawarar a shekarar 2022. Ya jaddada cewa, shigar Aljeriya cikin shawarar ba karfafa hadin gwiwar moriyar juna tsakaninta da Sin kadai zai yi ba, har ma da karawa tattalin arzikinta kuzarin bunkasuwa. (Fa’iza Mustapha, Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp